< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Una canción. Un Salmo de David. Mi corazón está firme, Dios. Cantaré y haré música con mi alma.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
¡Despertad, arpa y lira! Despertaré al amanecer.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Te daré gracias, Yahvé, entre las naciones. Te cantaré alabanzas entre los pueblos.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Porque tu bondad es grande sobre los cielos. Tu fidelidad llega a los cielos.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
¡Sé exaltado, Dios, por encima de los cielos! Que tu gloria sea sobre toda la tierra.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Para que tu amado sea liberado, salva con tu mano derecha, y respóndenos.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dios ha hablado desde su santuario: “En triunfo, Dividiré Siquem, y mediré el valle de Sucot.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Galaad es mía. Manasés es mío. Efraín también es mi casco. Judá es mi cetro.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab es mi lavadero. Lanzaré mi sandalia sobre Edom. Gritaré sobre Filistea”.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
¿Quién me llevará a la ciudad fortificada? ¿Quién me llevará a Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
¿No nos has rechazado, Dios? No sales, Dios, con nuestros ejércitos.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Danos ayuda contra el enemigo, porque la ayuda del hombre es vana.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
A través de Dios, nosotroslo haremos con valentía, ya que es él quien va a pisotear a nuestros enemigos.