< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Una canción. Un salmo de David. ¡Oh, Dios! ¡He confiado plenamente en ti! ¡Todo mi ser canta alabanzas a tu nombre!
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
¡Levántense, arpa y lira! ¡Despertaré al amanecer!
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Te agradeceré entre los pueblos, Señor, cantaré alabanzas a ti entre las naciones.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Porque tu gran amor llega más alto que los cielos, tu fidelidad es más grande que las nubes.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Dios, tu grandeza sobrepasa los cielos, y tu gloria está sobre toda la tierra.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
¡Rescata a los que amas! Respóndenos, y sálvanos con tu poder!
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dios ha hablado desde su Templo: “He dividido triunfantemente a Siquem y parte del Valle de Sucot.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Tanto Gilead como Manasés me pertenecen. Efraín es mi casco, y Judá es mi cetro.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Trataré a Moab como mi lavabo; pondré mi sandalia sobre Edom; gritaré en triunfo sobre Filistea”.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
¿Quién me traerá a la ciudad fortificada? ¿Quién me guiará a Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
¿Nos has rechazado, Dios? ¿No dirigirás a tus ejércitos nunca más?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Bríndanos, por favor, una mano de ayuda en contra de nuestros enemigos, porque la ayuda humana no vale la pena.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Nuestra fuerza está en Dios, y él destruirá a nuestros enemigos.

< Zabura 108 >