< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Pesem in psalm Davidov. Z radostnim srcem svojim, o Bog, bodem pel in prepeval, tudi slava moja.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Vstanite, brenklje in citre; zbudim se sè zarijo.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Slavil te bodem med ljudstvi, Gospod; in prepeval ti bodem med narodi:
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Velika je nad nebesa milost tvoja, in noter do gornjih oblakov resnica tvoja.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Povzdigni se nad nebesa, o Bog; in čez vso zemljo slava tvoja!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Da se rešijo izvoljeni tvoji, pomagaj z desnico svojo in usliši me.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Bog jo govoril po svetosti svoji; radoval se bodem, v dél dobodem Sihem, in dolino Sukotsko merim.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Moj je Gilead, moj Manase, in Efrajm moč glave moje, Juda poveljnik moj.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab umivalnik moj; čez Edom vržem svoj čevelj; proti Palestini bodem ukal.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Kdo me popelje v utrjeno mesto, kdo me popelje do Edoma?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Ali nisi bil ti, o Bog, zavrgel nas? da nisi hodil, o Bog, med našimi vojskami?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Daj nam pomoč zoper sovražnika; drugače je ničevost pomoč človeška.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
V Bogu delajmo vrlo, in on bode poteptal sovražnike naše.