< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Mon cœur est disposé, ô Dieu! je chanterai, je psalmodierai; c'est ma gloire.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Réveillez-vous, mon luth et ma harpe! Je devancerai l'aurore.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Je te louerai parmi les peuples, ô Éternel; je te célébrerai parmi les nations.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Car ta bonté s'élève au-dessus des cieux, et ta fidélité jusqu'aux nues.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
O Dieu, élève-toi sur les cieux! Que ta gloire soit sur toute la terre,
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Afin que tes bien-aimés soient délivrés. Sauve-moi par ta droite, et m'exauce!
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dieu a parlé dans son sanctuaire; je me réjouirai; je partagerai Sichem, je mesurerai la vallée de Succoth.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Galaad est à moi, à moi Manassé; Éphraïm est le rempart de ma tête, et Juda mon législateur.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab est le bassin où je me lave; je jette mon soulier sur Édom; je pousse des cris de joie sur le pays des Philistins.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Qui me conduira dans la ville forte? Qui me mènera jusqu'en Édom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
N'est-ce pas toi, ô Dieu, qui nous avais rejetés, et qui ne sortais plus, ô Dieu, avec nos armées?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Donne-nous du secours pour sortir de détresse; car la délivrance qui vient de l'homme n'est que vanité.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Nous ferons des actions de valeur en Dieu, et il foulera nos ennemis.