< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Cantique et psaume de David. Mon cœur est prêt, ô Dieu, mon cœur est prêt; je vais chanter des psaumes en ma gloire.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Réveillez-vous, ma harpe et ma cithare; je me lèverai dès l'aurore.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Seigneur, je te rendrai gloire parmi les peuples; je te chanterai des psaumes parmi les Gentils.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Car ta miséricorde est plus grande que les cieux; et ta vérité va jusqu'aux nues.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Dieu, sois exalté au-dessus des cieux; que ta gloire soit répandue sur toute la terre!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Afin que tes bien-aimés soient délivrés, sauve-moi par ta droite, et exauce-moi.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dieu a parlé dans son sanctuaire; je me réjouirai, et je partagerai Sichem, et je mesurerai le val des Tabernacles.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
A moi est Galaad, à moi Manassé; Ephraïm est l'appui de ma tête; Juda est mon roi,
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Et Moab le vase de mon espérance. Je poserai ma sandale sur l'Idumée, les étrangers me sont soumis.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Qui me ramènera dans la ville forte? Qui me guidera jusqu'à la terre d'Édom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
N'est-ce pas toi, ô Dieu, qui nous avais repoussés; ô Dieu, toi qui ne sortais plus à la tête de nos armées?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Donne-nous ton secours pour nous tirer de la tribulation; car il est vain, le salut qui vient de l'homme.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
En Dieu nous mettons notre force, et lui-même réduira à néant nos ennemis.

< Zabura 108 >