< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Cantique. Psaume de David. Mon cœur reste ferme, ô Dieu! Je puis chanter, célébrer tes louanges; c’est là mon honneur.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Réveillez-vous, ô luth et harpe! Je veux réveiller l’aurore.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Je te louerai parmi les nations, ô Seigneur, je te chanterai parmi les peuples.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Car ta grâce s’élève par-dessus les cieux, et ta bonté atteint jusqu’au firmament.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Montre ta grandeur, ô Dieu, qui dépasse les cieux; que ta gloire brille sur toute la terre!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Afin que tes bien-aimés échappent au danger, secours-nous avec ta droite, et exauce-moi!
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
L’Eternel l’a annoncé en son sanctuaire: "Je triompherai, je veux m’adjuger Sichem, mesurer au cordeau la vallée de Souccot.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
A moi Galaad! à moi Manassé! Ephraïm est la puissante sauvegarde de ma tête, Juda est mon sceptre.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab est le bassin où je me lave; sur Edom, je jette ma sandale, je triomphe du pays des Philistins."
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Qui me conduira à la ville forte? Qui saura me mener jusqu’à Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Ne sera-ce pas toi, ô Dieu, toi qui nous avais délaissés, qui ne faisais plus campagne avec nos armées?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Prête-nous secours contre l’adversaire, puisque trompeuse est l’aide de l’homme.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Avec Dieu, nous ferons des prouesses: c’est lui qui écrasera nos ennemis.