< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
Cantique. Psaume de David. Mon cœur est affermi, ô Dieu! je chanterai, et je psalmodierai, … mon âme aussi.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Éveillez-vous, luth et harpe! Je m’éveillerai à l’aube du jour.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Je te célébrerai parmi les peuples, ô Éternel! et je chanterai tes louanges parmi les peuplades;
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
Car ta bonté est grande par-dessus les cieux, et ta vérité [atteint] jusqu’aux nues.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Élève-toi, ô Dieu! au-dessus des cieux, et que ta gloire soit au-dessus de toute la terre.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Afin que tes bien-aimés soient délivrés, sauve par ta droite, et réponds-moi.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Dieu a parlé dans sa sainteté: je me réjouirai; je partagerai Sichem et je mesurerai la vallée de Succoth.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Galaad est à moi, Manassé est à moi, et Éphraïm est la force de ma tête; Juda est mon législateur;
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab est le bassin où je me lave; sur Édom j’ai jeté ma sandale; sur la Philistie je pousserai des cris de triomphe.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Qui me conduira dans la ville forte? Qui me mènera jusqu’en Édom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Ne sera-ce pas toi, ô Dieu, qui nous as rejetés, et qui n’es pas sorti, ô Dieu, avec nos armées?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Donne-nous du secours pour sortir de détresse; car la délivrance qui vient de l’homme est vaine.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Par Dieu nous ferons des actes de valeur, et c’est lui qui foulera nos adversaires.