< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
A song, a psalm of David. My heart is fixed, God; I will sing, yes, I will sing praises also with my honored heart.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Wake up, lute and harp; I will wake up the dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will give thanks to you, Yahweh, among the peoples; I will sing praises to you among the nations.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For your covenant faithfulness is great above the heavens; and your trustworthiness reaches to the skies.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Be exalted, God, above the heavens, and may your glory be exalted over all the earth.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
So that those you love may be rescued, rescue us with your right hand and answer me.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God has spoken in his holiness; “I will rejoice; I will divide Shechem and apportion out the Valley of Succoth.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead is mine, and Manasseh is mine; Ephraim also is my helmet; Judah is my scepter.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab is my washbasin; over Edom I will throw my shoe; I will shout in triumph because of Philistia.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who will bring me into the strong city? Who will lead me to Edom?”
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
God, have you not rejected us? You do not go into battle with our army.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us help against the enemy, for man's help is futile.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
We will triumph with God's help; he will trample down our enemies.