< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
A song a psalm of David. [is] steadfast Heart my O God I will sing and I will sing praises also honor my.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Awake! O lyre and harp I will waken [the] dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will give thanks you among the peoples - O Yahweh and I will sing praises to you not nations.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For [is] great above [the] heavens covenant loyalty your and [is] to [the] clouds faithfulness your.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Be exalted! above [the] heavens O God and [be] over all the earth glory your.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
So that they may be rescued! beloved [ones] your save! right [hand] your and answer me.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God - he has spoken in sanctuary his I will triumph I will divide up Shechem and [the] Valley of Succoth I will measure off.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
[belongs] to Me Gilead - [belongs] to me Manasseh and Ephraim [is] [the] protection of head my Judah [is] commander's staff my.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab - [is] [the] pot of washing my over Edom I throw sandal my over Philistia I shout in triumph.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who? will he bring me a city of fortification who? will he lead me to Edom.
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
¿ Not O God have you rejected us and not you go out O God with armies our.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give! to us help from [the] foe and [is] worthlessness [the] deliverance of humankind.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
In God we will do strength and he he will tread down opponents our.

< Zabura 108 >