< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
My heart is steadfast, God. I will sing zahmar ·musical praise· and I will give kavod ·weighty glory·.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Wake up, harp and lyre! I will wake up the dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will yadah ·extend hands in thankful praise· to you, Adonai, among the nations. I will sing zahmar ·musical praise· to you among the peoples.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For your chesed ·loving-kindness· is great above the heavens. Your faithfulness reaches to the skies.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Be exalted, God, above the heavens! Let your kavod ·weighty glory· be over all the earth.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
That your yadid ·beloved· may be delivered, save with your right hand, and answer us.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God has spoken from his sanctuary: “In triumph, I will divide Shechem, and measure out the valley of Sukkot.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead is mine. Manasseh [Causing to forget] is mine. Ephraim [Fruit] also is my helmet. Judah [Praised] is my scepter.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab [From father] is my wash pot. I will toss my sandal on Edom [Red]. I will shout over Philistia.”
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who will bring me into the fortified city? Who has led me to Edom [Red]?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Haven’t you rejected us, God? You don’t go out, God, with our armies.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us help against the enemy, for the help of man is vain.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Through God, we will do valiantly. For it is he who will tread down our enemies.

< Zabura 108 >