< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
“A psalm of David.” O God! my heart is strengthened! I will sing and give thanks.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Awake, my soul! awake, my psaltery and harp! I will wake with the early dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will praise thee, O LORD! among the nations; I will sing to thee among the peoples!
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For thy mercy reacheth to the heavens, And thy truth above the clouds.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Exalt thyself, O God! above the heavens, And thy glory above all the earth!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
That thy beloved ones may be delivered, Save with thy right hand, and answer me!
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God promiseth in his holiness; I will rejoice; I shall yet divide Shechem, And measure out the valley of Succoth;
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead shall be mine, and mine Manasseh; Ephraim shall be my helmet, And Judah my sceptre.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab shall be my washbowl; Upon Edom shall I cast my shoe; I shall triumph over Philistia.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who will bring me to the strong city? Who will lead me into Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Wilt not thou, O God! who didst forsake us, Who didst not go forth with our armies?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us thine aid in our distress, For vain is the help of man!
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Through God we shall do valiantly; For he will tread down our enemies.

< Zabura 108 >