< Zabura 108 >

1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
A Song, a Psalm of David. My heart is steadfast, O God; I will sing, yea, I will sing praises, even with my glory.
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Awake, psaltery and harp; I will awake the dawn.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
I will give thanks unto Thee, O LORD, among the peoples; and I will sing praises unto Thee among the nations.
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
For Thy mercy is great above the heavens, and Thy truth reacheth unto the skies.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Be Thou exalted, O God, above the heavens; and Thy glory be above all the earth.
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
That Thy beloved may be delivered, save with Thy right hand, and answer me.
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
God spoke in His holiness, that I would exult; that I would divide Shechem, and mete out the valley of Succoth.
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
Gilead is mine, Manasseh is mine; Ephraim also is the defence of my head; Judah is my sceptre.
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab is my washpot; upon Edom do I cast my shoe; over Philistia do I cry aloud.
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Who will bring me into the fortified city? Who will lead me unto Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Hast not Thou cast us off, O God? and Thou goest not forth, O God, with our hosts?
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Give us help against the adversary; for vain is the help of man.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Through God we shall do valiantly; for He it is that will tread down our adversaries.

< Zabura 108 >