< Zabura 108 >
1 Waƙa ce. Zabura ta Dawuda. Zuciyata tsayayyiya ce, ya Allah; zan rera in kuma yi kiɗi da dukan raina.
(En Sang. En Salme af David.) Mit Hjerte er trøstigt, Gud, mit hjerte er trøstigt; jeg vil synge og lovprise dig, vågn op, min Ære!
2 Ku farka, garaya da molo! Zan farkar da rana.
Harpe og Citer, vågn op, jeg vil vække Morgenrøden.
3 Zan yabe ka, ya Ubangiji, a cikin al’ummai; zan rera game da kai cikin mutane.
Jeg vil takke dig, HERRE, blandt Folkeslag, lovprise dig blandt Folkefærd;
4 Gama ƙaunarka da girma take, bisa fiye da sammai; amincinka ya kai sarari.
thi din Miskundhed når til Himlen, din Sandhed til Skyerne.
5 A ɗaukaka ka, ya Allah, a bisa sammai, bari kuma ɗaukakarka ta kasance a bisa dukan duniya.
Løft dig, o Gud, over Himlen, din Herlighed være over al Jorden!
6 Ka cece mu ka kuma taimake mu da hannunka na dama, domin waɗanda kake ƙauna su kuɓuta.
Til Frelse for dine elskede hjælp med din højre, bønhør os!
7 Allah ya yi magana daga wurinsa mai tsarki, “Ciki nasara zan raba Shekem in kuma auna Kwarin Sukkot.
Gud talede i sin Helligdom: "Jeg vil udskifte Sikem med Jubel, udmåle Sukkots Dal;
8 Gileyad nawa ne, Manasse nawa ne; Efraim shi hulan kwanona, Yahuda ne sandana na sarauta.
mit er Gilead, mit er Manasse, Efraim er mit Hoveds Værn, Juda min Herskerstav,
9 Mowab shi ne kwanon wankina, a kan Edom zan jefa takalmina; a bisa Filistiya zan yi kirari cikin nasara.”
Moab min Vaskeskål, på Edom kaster jeg min Sko, over Filisterland jubler jeg."
10 Wa zai kawo ni birni mai katanga? Wa zai jagorance ni zuwa Edom?
Hvo bringer mig til den befæstede By, hvo leder mig hen til Edom?
11 Ba kai ba ne, ya Allah, kai da ka ƙi mu ba ka kuwa fita tare da mayaƙanmu?
Har du ikke, Gud, stødt os fra dig? Du ledsager ej vore Hære.
12 Ka ba mu taimako a kan abokin gāba, gama taimakon mutum banza ne.
Giv os dog Hjælp mod Fjenden! Blændværk er Menneskers Støtte.
13 Tare da Allah za mu yi nasara, zai kuma tattaka abokan gābanmu.
Med Gud skal vi øve vældige Ting, vore Fjender træder han ned!