< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
„Дякуйте Господу, добрий бо Він, бо наві́ки Його милосердя!“
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
хай так скажуть ті всі, що Госпо́дь урятував їх, що ви́зволив їх з руки ворога,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
і з країв їх зібрав, — від сходу й захо́ду, від пі́вночі й моря!
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Блудили вони по пустині дорогою голою, осілого міста не знахо́дили,
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
голодні та спра́гнені, і в них їхня душа омліва́ла.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
І в недолі своїй вони Го́спода кли́кали, і Він визволяв їх від у́тисків їхніх!
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
І Він їх попрова́див дорогою про́стою, щоб до міста осілого йшли.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Нехай же подя́ку складу́ть Господе́ві за милість Його, та за чу́да Його синам лю́дським,
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
бо наси́тив Він спра́гнену Душу, а душу голодну напо́внив добром!
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Ті, хто перебував був у те́мряві та в сме́ртній ті́ні, то в'я́зні біди та заліза,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
бо вони спротивля́лися Божим слова́м, і відки́нули раду Всевишнього.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Та Він упокори́в їхнє серце терпі́нням, спіткну́лись вони — і ніхто не поміг,
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
і в недолі своїй вони Господа кли́кали, і Він визволя́в їх від у́тисків їхніх!
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
І Він вивів їх з те́мряви й мо́року, їхні ж кайда́ни сторо́щив.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Нехай же подяку складуть Господе́ві за милість Його, та за чу́да Його синам лю́дським,
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
бо Він полама́в мідні двері, і засу́ви залізні зрубав!
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Нерозумні страждали за грішну дорогу свою й за свої беззаконня.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Душа їхня від усякої їжі відве́рталася, — і дійшли вони аж до брам смерти,
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
і в недолі своїй вони Господа кли́кали, і Він визволяв їх від у́тисків їхніх, —
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Він послав Своє слово та їх уздоро́вив, і їх урятував з їхньої хвороби!
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Нехай же подяку складуть Господе́ві за милість Його та за чу́да Його синам лю́дським,
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
і хай жертви подяки прино́сять, і хай розповіда́ють зо співом про чи́ни Його!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Ті, хто по морю пливе́ корабля́ми, хто чинить зайняття своє на великій воді, —
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
вони бачили чи́ни Госпо́дні та чу́да Його в глибині!
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Він скаже — і буря зривається, і підно́сяться хвилі Його,
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
до неба вони підійма́ються, до безодні спада́ють, — у небезпеці душа їхня хвилюється!
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Вони крутяться й ходять вперед та назад, як п'яни́й, і вся́ їхня мудрість бенте́житься!
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Та в недолі своїй вони Господа кликали, і Він визволяв їх від у́тисків їхніх!
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Він змінює бурю на ти́шу, — і стихають їхні хвилі,
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
і раділи, що вти́хли вони, і Ві́н їх привів до бажа́ної при́стані.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Нехай же подяку складуть Господе́ві за милість, та за чу́да Його синам лю́дським!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Нехай величають Його на наро́дньому зборі, і нехай вихваля́ють Його на засі́данні старших!
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Він обе́ртає рі́чки в пустиню, а водні джере́ла — на суході́л,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
плодю́чу землю — на солонча́к через зло́бу мешка́нців її.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Він пустиню обе́ртає в водне болото, а землю суху́ — в джерело́,
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
і голодних садо́вить Він там, а вони ставлять місто на ме́шкання,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
і поля́ засіва́ють, і виногра́дники са́дять, — і отримують плід урожа́ю!
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
І благословляє Він їх, — і сильно розмно́жуються, і оде́ржують плід урожа́ю!
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Та змаліли вони й похили́лися з утиску злого та з сму́тку.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Виливає Він га́ньбу на можних, — і блу́дять вони без дороги в пустині,
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
а вбогого Він підіймає з убо́зтва, і розмно́жує роди, немов ту ота́ру.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Це бачать правдиві й радіють, і закриває уста́ свої всяке безправ'я.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Хто мудрий, той все це завва́жить, — і пізна́ють вони́ милосердя Господнє!