< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Tacken HERREN, ty han är god, ty hans nåd varar evinnerligen.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Så säge HERRENS förlossade, de som han har förlossat ur nöden,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
de som han har församlat ifrån länderna, från öster och från väster, från norr och från havssidan.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
De irrade omkring i öknen på öde stigar, de funno ingen stad där de kunde bo;
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
de hungrade och törstade, deras själ försmäktade i dem.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Men de ropade till HERREN i sin nöd, och han räddade dem ur deras trångmål.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Och han ledde dem på en rätt väg, så att de kommo till en stad där de kunde bo.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
De må tacka HERREN för hans nåd och för hans under med människors barn,
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
att han mättade den försmäktande själen och uppfyllde den hungrande själen med sitt goda.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
De sutto i mörker och dödsskugga, fångna i elände och järnbojor,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
därför att de hade varit gensträviga mot Guds ord och hade föraktat den Högstes råd.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Han kuvade deras hjärtan med olycka; de kommo på fall och hade ingen hjälpare.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Men de ropade till HERREN i sin nöd, och han frälste dem ur deras trångmål;
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
han förde dem ut ur mörkret och dödsskuggan, och deras bojor slet han sönder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
De må tacka HERREN för hans nåd och för hans under med människors barn,
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
att han krossade kopparportarna och bröt sönder järnbommarna.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
De voro oförnuftiga, ty de vandrade i överträdelse, och blevo nu plågade för sina missgärningars skull;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
deras själ vämjdes vid all mat, och de voro nära dödens portar.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Men de ropade till HERREN i sin nöd, och han frälste dem ur deras trångmål.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Han sände sitt ord och botade dem och räddade dem från graven.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
De må tacka HERREN för hans nåd och för hans under med människors barn;
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
de må offra lovets offer och förtälja hans verk med jubel.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
De foro på havet med skepp och drevo sin handel på stora vatten;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
där fingo de se HERRENS gärningar och hans under på havsdjupet.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Med sitt ord uppväckte han stormvinden, så att den hävde upp dess böljor.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
De foro upp mot himmelen, ned i djupen; deras själ upplöstes av ångest.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
De raglade och stapplade såsom druckna, och all deras vishet blev till intet.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Men de ropade till HERREN i sin nöd, och han förde dem ut ur deras trångmål.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Han förbytte stormen i lugn, så att böljorna omkring dem tystnade.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Och de blevo glada att det vart stilla, och han förde dem till den hamn dit de ville.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
De må tacka HERREN för hans nåd och för hans under med människors barn;
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
de må upphöja honom i folkets församling och lova honom där de äldste sitta.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Han gjorde strömmar till öken, källsprång till torr mark,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
bördigt land till salthed, för dess inbyggares ondskas skull.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Han gjorde öknen till en vattenrik sjö och torrt land till källsprång.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Och han lät de hungrande bo där, och de byggde en stad där de kunde bo.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
De besådde åkrar och planterade vingårdar, som gåvo dem sin frukt i avkastning.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Han välsignade dem, och de förökades storligen, och deras boskapshjordar lät han icke förminskas.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Väl blevo de sedan ringa och nedböjda, i det olycka och bedrövelse tryckte dem,
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
men han som utgjuter förakt över furstar och låter dem irra omkring i väglösa ödemarker,
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
han upphöjde då den fattige ur eländet och lät släkterna växa till såsom fårhjordar.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
De redliga se det och glädja sig, och all orättfärdighet måste tillsluta sin mun.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Den som är vis, han akte härpå och besinne HERRENS nådegärningar.

< Zabura 107 >