< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alabe al Señor, porque él es bueno; porque su misericordia es inmutable para siempre.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Deje que aquellos cuya causa ha tomado el Señor lo digan, su pueblo a quien él ha quitado de las manos de sus enemigos;
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Haciéndolos venir juntos de todas las tierras, del este y del oeste, del norte y del sur.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Ellos vagabundeaban en los lugares baldíos; no vieron camino a un lugar de descanso.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Sus almas se debilitaron por la necesidad de comida y bebida.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Entonces enviaron su clamor al Señor en su dolor, y él les dio la salvación de todos sus problemas;
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Guiándolos en el camino correcto, para que puedan entrar en la ciudad de su lugar de descanso.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
¡Que los hombres alaben al Señor por su misericordia y por las maravillas que hace por los hijos de los hombres!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Él le da su deseo al alma incontenible, para que esté lleno de cosas buenas.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Aquellos que estaban en la oscuridad, en la noche negra, en cadenas de tristeza;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Porque fueron contra las palabras de Dios, y no pensaron en las leyes del Altísimo:
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
De modo que hizo que sus corazones se cargaran de dolor; estaban cayendo, y no tenían ayuda.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Entonces enviaron su clamor al Señor en su dolor, y él les dio la salvación de todos sus problemas.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Los sacó de la oscuridad y la noche negra, y todas sus cadenas se rompieron.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
¡Que los hombres alaben al Señor por su misericordia y por las maravillas que hace por los hijos de los hombres!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Las puertas de bronce se rompen por su brazo, y las cintas de hierro se cortan en dos.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Los hombres necios, a causa de sus pecados, y por su maldad, se turbaron;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Están disgustados con todo alimento, y se acercan a las puertas de la muerte.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Entonces alzaron su clamor al Señor en su dolor, y él les dio la salvación de todos sus problemas.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Él envió su palabra y los hizo bien, y los mantuvo a salvo del inframundo.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
¡Que los hombres alaben al Señor por su misericordia y por las maravillas que hace por los hijos de los hombres!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Hagamos ofrendas de alabanza, dando noticias de sus obras con gritos de alegría.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Los que descienden al mar en barcos, que hacen negocios en las grandes aguas;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Ellos ven las obras del Señor y sus maravillas en lo profundo.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Porque a su palabra, sube el viento de la tempestad, levantando las olas.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Los marineros suben al cielo, y descienden al abismo; sus almas se desperdician debido a su problema.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Son convertidos aquí y allá, rodando como un hombre que está lleno de vino; y toda su sabiduría no llega a nada.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Entonces alzaron su clamor al Señor en su dolor, y él les dio la salvación de todos sus problemas.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Él convierte la tormenta en una calma, para que las olas estén en paz.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Entonces se alegran, porque el mar está quieto, y él los lleva al puerto de su deseo.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
¡Que los hombres alaben al Señor por su misericordia y por las maravillas que hace por los hijos de los hombres!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Dejen que le den gloria en la reunión del pueblo, y alabanza entre los jefes.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Hace ríos en lugares baldíos, y manantiales de agua en tierra seca;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
Él hace un país fértil en un desierto de sal, a causa de los pecados de los que viven allí.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Hace una tierra desierta en un lugar de agua, y una tierra seca en manantiales de agua.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Y allí él da a los pobres un lugar de descanso, para que puedan hacerse una ciudad;
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Y pon la semilla en los campos, y haz viñas para darles fruto.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Él les da su bendición para que sean aumentados grandemente, y su ganado no disminuya.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Y cuando son humillados, y abatidos por la tribulación y la tristeza,
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Él pone fin al orgullo de los reyes, y los envía vagando por las tierras baldías donde no hay camino.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Pero saca al pobre de sus problemas, y le da familias como un rebaño.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Los rectos lo ven y se alegran: la boca del pecador se detiene.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Los sabios reflexionen sobre estas cosas, y vean las misericordias del Señor.