< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
ALABAD á Jehová, porque es bueno; porque para siempre [es] su misericordia.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Dígan[lo] los redimidos de Jehová, los que ha redimido del poder del enemigo,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Y los ha congregado de las tierras, del oriente y del occidente, del aquilón y de la mar.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Anduvieron perdidos por el desierto, por la soledad sin camino, no hallando ciudad de población.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hambrientos y sedientos, su alma desfallecía en ellos.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Habiendo empero clamado á Jehová en su angustia, librólos de sus aflicciones:
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Y dirigiólos por camino derecho, para que viniesen á ciudad de población.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Alaben la misericordia de Jehová, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Porque sació al alma menesterosa, y llenó de bien al alma hambrienta.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Los que moraban en tinieblas y sombra de muerte, aprisionados en aflicción y en hierros;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Por cuanto fueron rebeldes á las palabras de Jehová, y aborrecieron el consejo del Altísimo,
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Por lo que quebrantó él con trabajo sus corazones, cayeron y no hubo quien [les] ayudase;
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Luego que clamaron á Jehová en su angustia, librólos de sus aflicciones.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Sacólos de las tinieblas y de la sombra de muerte, y rompió sus prisiones.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Alaben la misericordia de Jehová, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Porque quebrantó las puertas de bronce, y desmenuzó los cerrojos de hierro.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Los insensatos, á causa del camino de su rebelión y á causa de sus maldades, fueron afligidos.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Su alma abominó toda vianda, y llegaron hasta las puertas de la muerte.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Mas clamaron á Jehová en su angustia, y salvólos de sus aflicciones.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Envió su palabra, y curólos, y librólos de su ruina.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Alaben la misericordia de Jehová, y sus maravillas para con los hijos de los hombres:
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Y sacrifiquen sacrificios de alabanza, y publiquen sus obras con júbilo.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Los que descienden á la mar en navíos, y hacen negocio en las muchas aguas,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Ellos han visto las obras de Jehová, y sus maravillas en el profundo.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
El dijo, é hizo saltar el viento de la tempestad, que levanta sus ondas.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Suben á los cielos, descienden á los abismos: sus almas se derriten con el mal.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Tiemblan, y titubean como borrachos, y toda su ciencia es perdida.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Claman empero á Jehová en su angustia, y líbralos de sus aflicciones.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Hace parar la tempestad en sosiego, y se apaciguan sus ondas.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Alégranse luego porque se reposaron; y él los guía al puerto que deseaban.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Alaben la misericordia de Jehová, y sus maravillas para con los hijos de los hombres.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Y ensálcenlo en la congregación del pueblo; y en consistorio de ancianos lo alaben.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
El vuelve los ríos en desierto, y los manantiales de las aguas en secadales;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
La tierra fructífera en salados, por la maldad de los que la habitan.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Vuelve el desierto en estanques de aguas, y la tierra seca en manantiales.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Y allí aposenta á los hambrientos, y disponen ciudad para habitación;
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Y siembran campos, y plantan viñas, y rinden crecido fruto.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Y los bendice, y se multiplican en gran manera; y no disminuye sus bestias.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Y luego son menoscabados y abatidos á causa de tiranía, de males y congojas.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
El derrama menosprecio sobre los príncipes, y les hace andar errados, vagabundos, sin camino:
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Y levanta al pobre de la miseria, y hace [multiplicar] las familias como [rebaños de] ovejas.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Vean los rectos, y alégrense; y toda maldad cierre su boca.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
¿Quién es sabio y guardará estas cosas, y entenderá las misericordias de Jehová?