< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Хвалите Господа, јер је добар; јер је довека милост Његова.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Тако нека кажу које је избавио Господ, које је избавио из руке непријатељеве,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Скупио их из земаља, од истока и запада, од севера и мора.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Луташе по пустињи где се не живи, пута граду насељеном не находише;
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Беху гладни и жедни, и душа њихова изнемагаше у њима;
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Али завикаше ка Господу у тузи својој; и избави их из невоље њихове.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
И изведе их на прав пут, који иде у град насељени.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Јер сити душу ташту, и душу гладну пуни добра.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Седеше у тами и у сену смртном, оковани у тугу и у гвожђе;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Јер не слушаше речи Божијих, и не марише за вољу Вишњег.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Он поништи срце њихово страдањем; спотакоше се, и не беше кога да помогне.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Али завикаше ка Господу у тузи својој, и избави их из невоље њихове;
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Изведе их из таме и сена смртног, и раскиде окове њихове.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Јер разби врата бронзана, и преворнице гвоздене сломи.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Безумници страдаше за неваљале путеве своје, и за неправде своје.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Свако се јело гадило души њиховој, и дођоше до врата смртних.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Али завикаше ка Господу у тузи својој, и избави их из невоље њихове.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Посла реч своју и исцели их, и избави их из гроба њиховог.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
И нека принесу жртву за хвалу, и казују дела Његова у песмама!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Који плове по мору на корабљима, и раде на великим водама,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Они су видели дела Господња, и чудеса Његова у дубини.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Каже, и диже се силан ветар, и устају вали на њему,
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Дижу се до небеса и спуштају до бездана: душа се њихова у невољи разлива;
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Посрћу и љуљају се као пијани; све мудрости њихове нестаје.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Али завикаше ка Господу у тузи својој, и изведе их из невоље њихове.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Он обраћа ветар у тишину, и вали њихови умукну.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Веселе се кад се стишају, и води их у пристаниште које желе.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Нека хвале Господа за милост Његову, и за чудеса Његова ради синова људских!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Нека Га узвишују на сабору народном, на скупштини старешинској славе Га!
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Он претвара реке у пустињу, и изворе водене у сухоту,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
Родну земљу у слану пустару за неваљалство оних који живе на њој.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Он претвара пустињу у језера, и суву земљу у изворе водене,
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
И насељава онамо гладне. Они зидају градове за живљење;
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Сеју поља, саде винограде и сабирају летину.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Благосиља их и множе се јако, и стоке им не умањује.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Пре их беше мало, падаху од зла и невоље, што их стизаше.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Он сипа срамоту на кнезове, и оставља их да лутају по пустињи где нема путева.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Он извлачи убогога из невоље, и племена множи као стадо.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Добри виде и радују се, а свако неваљалство затискује уста своја.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Ко је мудар, нека запамти ово, и нека познају милости Господње.