< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Louvae ao Senhor, porque elle é bom, porque a sua benignidade dura para sempre.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Digam-n'o os remidos do Senhor, os que remiu da mão do inimigo,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
E os que congregou das terras do oriente e do occidente, do norte e do sul.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Andaram desgarrados pelo deserto, por caminhos solitarios; não acharam cidade para habitarem.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Famintos e sedentos, a sua alma n'elles desfallecia.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
E clamaram ao Senhor na sua angustia, e os livrou das suas necessidades.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
E os levou por caminho direito, para irem a uma cidade de habitação.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Louvem ao Senhor pela sua bondade, e pelas suas maravilhas para com os filhos dos homens.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Pois fartou a alma sedenta, e encheu de bondade a alma faminta.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Tal como a que se assenta nas trevas e sombra da morte, presa em afflicção e em ferro;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Porquanto se rebellaram contra as palavras de Deus, e desprezaram o conselho do Altissimo,
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Portanto lhes abateu o coração com trabalho; tropeçaram, e não houve quem os ajudasse.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Então clamaram ao Senhor na sua angustia, e os livrou das suas necessidades.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Tirou-os das trevas e sombra da morte; e quebrou as suas prisões.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Louvem ao Senhor pela sua bondade, e pelas suas maravilhas para com os filhos dos homens.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Pois quebrou as portas de bronze; e despedaçou os ferrolhos de ferro.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Os loucos, por causa da sua transgressão, e por causa das suas iniquidades, são afflictos.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
A sua alma aborreceu toda a comida, e chegaram até ás portas da morte.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Então clamaram ao Senhor na sua angustia: e elle os livrou das suas necessidades.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Enviou a sua palavra, e os sarou; e os livrou da sua destruição.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Louvem ao Senhor pela sua bondade, e pelas suas maravilhas para com os filhos dos homens.
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
E offereçam os sacrificios de louvor, e relatem as suas obras com regozijo.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Os que descem ao mar em navios, mercando nas grandes aguas,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Esses vêem as obras do Senhor, e as suas maravilhas no profundo.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Pois elle manda, e se levanta o vento tempestuoso, que eleva as suas ondas.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Sobem aos céus; descem aos abysmos, e a sua alma se derrete em angustias.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Andam e cambaleam como ebrios, e perderam todo o tino.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Então clamam ao Senhor na sua angustia; e elle os livra das suas necessidades.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Faz cessar a tormenta, e calam-se as suas ondas.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Então se alegram, porque se aquietaram; assim os leva ao seu porto desejado.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Louvem ao Senhor pela sua bondade, e pelas suas maravilhas para com os filhos dos homens.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Exaltem-n'o na congregação do povo, e glorifiquem-n'o na assembléa dos anciãos.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Elle converte os rios em um deserto, e as fontes em terra sedenta:
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
A terra fructifera em esteril, pela maldade dos que n'ella habitam.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Converte o deserto em lagoa, e a terra secca em fontes.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
E faz habitar ali os famintos, para que edifiquem cidade para habitação;
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
E semeiam os campos e plantam vinhas, que produzem fructo abundante.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Tambem os abençoa, de modo que se multiplicam muito; e o seu gado não diminue.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Depois se diminuem e se abatem, pela oppressão, afflicção e tristeza.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Derrama o desprezo sobre os principes, e os faz andar desgarrados pelo deserto, onde não ha caminho.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Porém livra ao necessitado da oppressão em um logar alto, e multiplica as familias como rebanhos.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Os rectos o verão, e se alegrarão, e toda a iniquidade tapará a bocca.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Quem é sabio observará estas coisas, e elles comprehenderão as benignidades do Senhor.