< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Pris Herren, for han er god, hans miskunnhet varer evindelig.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Så sie Herrens gjenløste, de som han har gjenløst av nødens hånd,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
og som han har samlet fra landene, fra øst og fra vest, fra nord og fra havet.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
De fór vill i ørkenen, i et uveisomt øde, de fant ikke en by å bo i.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
De var hungrige og tørste, deres sjel vansmektet i dem.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Da ropte de til Herren i sin nød; av deres trengsler utfridde han dem,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
og han førte dem på rett vei, så de gikk til en by de kunde bo i.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
De skal prise Herren for hans miskunnhet og for hans undergjerninger mot menneskenes barn;
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
for han mettet den vansmektende sjel og fylte den hungrige sjel med godt.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
De satt i mørke og i dødsskygge, bundet i elendighet og jern,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
fordi de hadde vært gjenstridige mot Guds ord og foraktet den Høiestes råd.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Derfor bøide han deres hjerter ved lidelse; de snublet, og det var ikke nogen hjelper.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Da ropte de til Herren i sin nød; av deres trengsler frelste han dem.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Han førte dem ut av mørke og dødsskygge og rev sønder deres bånd.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
De skal prise Herren for hans miskunnhet og for hans undergjerninger mot menneskenes barn;
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
for han brøt sønder porter av kobber og hugg sønder bommer av jern.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
De var dårer og blev plaget for sin syndige vei og for sine misgjerninger;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
deres sjel vemmedes ved all mat, og de kom nær til dødens porter.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Da ropte de til Herren i sin nød; av deres trengsler frelste han dem.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Han sendte sitt ord og helbredet dem og reddet dem fra deres graver.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
De skal prise Herren for hans miskunnhet og for hans undergjerninger mot menneskenes barn;
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
og ofre takkoffere og fortelle om hans gjerninger med jubel.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
De som fór ut på havet i skib, som drev handel på store vann,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
de så Herrens gjerninger og hans underverker på dypet.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Han bød og lot det komme en stormvind, og den reiste dets bølger.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
De fór op imot himmelen, de fór ned i avgrunnene, deres sjel blev motløs i ulykken.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
De tumlet og vaklet som en drukken mann, og all deres visdom blev til intet.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Da ropte de til Herren i sin nød, og av deres trengsler førte han dem ut.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Han lot stormen bli til stille, og bølgene omkring dem tidde.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Og de gledet sig over at de la sig; og han førte dem til den havn de ønsket.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
De skal prise Herren for hans miskunnhet og for hans undergjerninger mot menneskenes barn
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
og ophøie ham i folkets forsamling og love ham der hvor de gamle sitter.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Han gjorde elver til en ørken og vannkilder til et tørstig land,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
et fruktbart land til et saltland for deres ondskaps skyld som bodde der.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Han gjorde en ørken til en vannrik sjø og et tørt land til vannkilder.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Og han lot de hungrige bo der, og de grunnla en by til å bo i.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Og de tilsådde akrer og plantet vingårder, og de vant den frukt de bar.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Og han velsignet dem, og de blev meget tallrike, og av fe gav han dem ikke lite.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Så minket de igjen og blev nedbøiet ved trengsel, ulykke og sorg.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Han som utøser forakt over fyrster og lar dem fare vill i et uveisomt øde,
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
han ophøiet den fattige av elendighet og gjorde slektene som hjorden.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
De opriktige ser det og gleder sig, og all ondskap lukker sin munn.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Den som er vis, han akte på dette og merke på Herrens nådegjerninger!