< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Célébrez l'Éternel; car il est bon, Et sa miséricorde dure éternellement!
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Ainsi parleront les rachetés de l'Éternel, Ceux qu'il a rachetés de la main de l'oppresseur,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Et qu'il a rassemblés de tous les pays, De l'Orient et de l'Occident, du Nord et du Midi.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Ils erraient dans le désert, sur un chemin solitaire; Ils ne trouvaient aucune ville qui pût leur servir de refuge.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Ils étaient affamés et altérés; Leur âme défaillait en eux.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Alors ils ont crié vers l'Éternel, dans leur détresse, Et il les a délivrés de leurs angoisses.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Il les a conduits par le droit chemin, Jusque dans une ville qu'ils ont habitée.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Qu'ils célèbrent donc la bonté de l'Éternel, Et ses miracles en faveur des enfants des hommes!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Car il a rassasié l'âme altérée. Et comblé de biens l'âme affamée.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
D'autres habitaient dans les ténèbres Et dans l'ombre de la mort; Ils étaient captifs et gémissaient dans les chaînes,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Pour avoir été rebelles aux paroles de Dieu, Et avoir méprisé le conseil du Très-Haut.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Il avait humilié leur coeur par la souffrance: Ils succombaient, sans que personne ne les secourût.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Alors ils ont crié vers l'Éternel, dans leur détresse, Et il les a délivrés de leurs angoisses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Il les a tirés des ténèbres et de l'ombre de la mort; Il a brisé leurs chaînes.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Qu'ils célèbrent donc la bonté de l'Éternel, Et ses miracles en faveur des enfants des hommes!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Car il a brisé les portes d'airain, Et rompu les barreaux de fer.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Insensés qu'ils étaient! Ils portaient la peine De leurs transgressions et de leurs iniquités;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Ils avaient en horreur toute nourriture; Ils touchaient aux portes de la mort.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Alors ils ont crié vers l'Éternel, dans leur détresse, Et il les a délivrés de leurs angoisses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Il a envoyé sa parole; il les a guéris, Et il les a retirés de leurs tombeaux.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Qu'ils célèbrent donc la bonté de l'Éternel, Et ses miracles en faveur des enfants des hommes!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Qu'ils offrent des sacrifices d'actions de grâces Et racontent ses oeuvres avec des chants de triomphe!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Ceux qui descendent sur la mer, dans des navires. Et qui trafiquent sur les grandes eaux,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Ceux-là voient les oeuvres de l'Éternel, Et ses merveilles dans les profondeurs de l'abîme.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Il parle, et il fait lever un vent de tempête, Qui soulève les vagues de la mer.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Ils montent aux cieux; ils descendent aux abîmes; Leur âme se fond d'angoisse.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Ils ensemencent des champs, et ils plantent des vignes, Qui portent des fruits abondants.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Alors ils ont crié vers l'Éternel, dans leur détresse, Et il les a délivrés de leurs angoisses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Il fait succéder le calme à la tempête, Et les vagues s'apaisent.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Ils se réjouissent de ce qu'elles sont calmées. Et Dieu les conduit au port qu'ils désiraient.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Qu'ils célèbrent donc la bonté de l'Éternel, Et ses miracles en faveur des enfants des hommes!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Qu'ils l'exaltent dans l'assemblée du peuple! Qu'ils le louent dans le conseil des anciens!
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
L'Éternel change les fleuves en désert, Les sources d'eau en un sol aride,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
Et la terre fertile en lande salée, A cause de la méchanceté de ses habitants.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Il change aussi le désert en étang, Et la terre aride en sources d'eau.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Il y fait habiter ceux qui étaient affamés: Ils fondent une ville pour y demeurer.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Ils ensemencent des champs, et ils plantent des vignes, Qui portent des fruits abondants.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Dieu les bénit: ils deviennent très nombreux, Et il ne laisse pas diminuer leur bétail.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
D'autres sont amoindris et humiliés Par l'oppression, le malheur et la souffrance.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
L'Éternel répand le mépris sur les grands. Et les fait errer dans un désert sans route.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Mais il délivre de leur affliction les malheureux, Et rend leurs familles nombreuses Comme de grands troupeaux.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
A cette vue, les justes sont remplis de joie; Mais tous les injustes ont la bouche fermée.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Que celui qui est sage prenne garde à ces choses. Et qu'il sache comprendre les bontés de l'Éternel!