< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to Yahweh, because he always does good [things for us] His faithful love [for us] lasts forever!
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Those whom Yahweh has saved should tell others that he has rescued them from their enemies.
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
He has gathered [those of you] who were [(exiled/taken forcefully)] to many lands; [he has gathered you together from] the east and the west, from the north and from the south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Some of those [who returned from those countries] wandered in the desert; they were lost and had no homes to live in.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
They were hungry and thirsty, and they were very discouraged.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
When they were in trouble, they called out to Yahweh, and he rescued them from (being distressed/their difficulties).
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
He led them along a straight road [where they walked safely] to cities [in Canaan] where they could live.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
They should praise/thank Yahweh for loving them faithfully and for the wonderful things that he does for people.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
He gives thirsty people plenty [of water] to drink, and he gives hungry people plenty of good things [to eat].
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Some of them were in very dark [HEN] (places [in Babylonia/other countries]); they were prisoners, suffering because of chains [fastened to their hands and feet].
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
They were in prison because they had (rebelled against/not obeyed) the message of God; they were there because they had despised the advice given by God, who is greater than all other gods.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
[That is why] their bodies were worn out from hard labor; when they fell down, there was no one who would help them.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
In their troubles, they called out to Yahweh, and he rescued them from their being distressed.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He broke the chains that were on their hands and feet; and brought them out of those very dark [prisons].
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
He broke down the [prison] gates that were made of bronze, and cut through the [prison] bars that were made of iron. [So they also] should praise/thank Yahweh for faithfully loving [them], and for [all] the wonderful things that he does for people.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Some of them foolishly rebelled [against God], so they suffered for their sins.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
They did not want to eat any food, and they almost died.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
In their troubles, they [also] called out to Yahweh, and he rescued them from their being distressed.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
When he commanded that they be healed, they were healed; he saved them from dying.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
They [also] should praise/thank Yahweh for faithfully loving them, and for [all] the wonderful things that he does for people.
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
They should give offerings to him to show that they are thankful, and they should sing joyfully about the miracles that he has performed.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Some of them sailed in ships; they were selling things [in ports] throughout the world.
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
[As they were sailing], they also saw the miracles that Yahweh performed, the wonderful things that he did [when they were] on very deep seas.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
He commanded the winds, and they became strong and (stirred up high waves/caused waves to rise high).
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
The ships [in which they were sailing] were tossed high in the air, and [then] they sank into the (troughs/low places) [between the high waves]; then the sailors were terrified.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They stumbled about and staggered like drunken men, and they did not know what to do.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
In their troubles, they [also] called out to Yahweh, and he rescued them from their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He (calmed the storm/caused the wind to stop blowing), and he caused the waves to completely subside.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
They were [very] glad when it became calm; and Yahweh brought them safely into a harbor.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
They [also] should praise/thank Yahweh for faithfully loving [them], and for [all] the wonderful things that he does for people.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
They should praise him among the [Israeli] people when they have gathered together, and they should praise him in front of the leaders [of the country].
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
[Sometimes] Yahweh causes rivers [to become dry], [with the result that the land] becomes a desert, and springs of water become dry land.
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
[Sometimes] he causes land that has produced lots of crops to become salty wastelands, [with the result that they do not produce crops]. He does that because the people who live there are [very] wicked.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
[But sometimes] he causes pools of water to appear in deserts, and he causes springs to flow in very dry ground.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
He brings hungry [people] into that land, to live there and build cities [there].
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
They plant seeds in their fields, and they plant grapevines that produce big crops [of grapes].
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
He blesses the people, and the women give birth to many children, and they have large herds of cattle.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
When the number of people becomes smaller and they have been humiliated [by their enemies] by being oppressed and caused to suffer [DOU],
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Yahweh shows contempt for the leaders who oppress them, and causes them to wander in deserts where there are no roads.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
But he rescues poor [people] from (being in misery/suffering), and causes their families [to increase in number] like flocks of sheep.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
Godly/Righteous [people will (see/hear about)] these things, and they will rejoice, and wicked people [will hear about these things, too], [but] they will have nothing to say in reply.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Those who are wise should think carefully about those things; they should consider [all the things] that Yahweh [has done to show that he] faithfully loves [them].