< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Give thanks to the Lord for his goodness for his kindness endures forever.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let this be the song of the ransomed, whom the Lord has redeemed from distress,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
gathering them from all lands, east, west, north, and south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
In the wastes of the desert some wandered, finding no way to a city inhabited.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Full of hunger and thirst, their spirit failed.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their trouble, and he saved them from their distresses,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
guiding them straight on the way, till they reached an inhabited city.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them thank the Lord for his kindness, for his wonderful deeds for people;
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
for the thirsty he satisfies, and the hungry he fills with good things.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Some sat in darkness and gloom prisoners in irons and misery,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
for rebelling against God’s word, and spurning the Most High’s counsel.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Their heart was bowed with toil; there was no one to help when they stumbled.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their trouble, and he saved them from their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Out of darkness and gloom he brought them, and burst their chains.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them praise the Lord for his kindness, for his wonderful deeds for people.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he shattered the gates of bronze, and broke bars of iron.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Some were sick from their wicked ways, and suffering because of their sins.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
All manner of food they hated; they had come to the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their trouble, and he saved them from their distresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sent his word and healed them, and delivered their life from the pit.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them praise the Lord for his kindness, for his wonderful deeds for people.
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Let them offer to him thankofferings, and with joy tell what things he has done.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Some crossed the sea in ships, doing business in great waters.
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
They have seen what the Lord can do, and his wonderful deeds on the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
At his command rose a tempest, which lifted the waves on high.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Up to heaven they went, down to the depths; their courage failed them.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They staggered and reeled like drunkards; all their skills useless.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their trouble, and he saved them from their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He stilled the storm to a whisper, and the waves of the sea were hushed.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
They were glad, because it was quiet; they were led to the haven they longed for.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them praise the Lord, for his kindness, for his wonderful deeds for people.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Where the people assemble, extol him, and praise him in council of elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turns streams into a wilderness, springs of water into thirsty land,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
fruitful land into a salt waste, because of the sin of the people.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
A desert he makes pools of water, a land of drought into springs of water.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
He settles the hungry therein, they establish a city to live in.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
They sow fields and plant vineyards, which furnish a fruitful yield.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
By his blessing they multiply greatly, and he lets not their cattle decrease.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Yet when they are bowed and diminished by oppression, misfortune, or sorrow,
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
he pours contempt upon princes, and on trackless wastes leads them astray
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
He lifts the poor out of misery, and makes families fruitful as flocks.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
At this sight shall the upright be glad, and all wicked mouths shall be stopped.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Let those who are wise observe this, and consider the love of the Lord