< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
“BOOK V.” O give thanks to the LORD, for he is good; For his mercy endureth for ever!
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let the redeemed of the LORD say it, Whom he hath redeemed from the hand of the enemy;
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Whom he hath gathered from the lands, From the east, the west, the north, and the south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They were wandering in the wilderness, in a desert, They found no way to a city to dwell in.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
They were hungry and thirsty, And their souls fainted within them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the LORD in their trouble, And he delivered them out of their distress.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
He led them in a straight way, Till they came to a city where they might dwell.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
O let them praise the LORD for his goodness, For his wonderful works to the children of men!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfieth the thirsty, And the hungry he filleth with good.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
They dwelt in darkness and the shadow of death, Being bound in affliction and iron;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Because they disobeyed the commands of God, And contemned the will of the Most High;
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Their hearts he brought down by hardship; They fell down, and there was none to help.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
But they cried to the LORD in their trouble, And he saved them out of their distresses;
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brought them out of darkness and the shadow of death, And brake their bands asunder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
O let them praise the LORD for his goodness, For his wonderful works to the children of men!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he hath broken the gates of brass, And cut the bars of iron asunder.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
The foolish, because of their transgressions, And because of their iniquities, were afflicted;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
They abhorred all kinds of food; They were near to the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the LORD in their trouble, And he delivered them out of their distresses;
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sent his word, and healed them, And saved them from their destruction.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
O let them praise the LORD for his goodness, For his wonderful works to the children of men!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Let them offer the sacrifices of thanksgiving, And declare his works with joy!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
They who go down to the sea in ships, And do business in great waters,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
These see the works of the LORD, And his wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
He commandeth, and raiseth the stormy wind, Which lifteth high the waves.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They mount up to the heavens, They sink down to the depths, Their soul melteth with distress;
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They reel and stagger like a drunken man, And all their skill is vain.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cry to the LORD in their trouble, And he saveth them out of their distresses;
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He turneth the storm into a calm, And the waves are hushed;
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Then they rejoice that they are still, And he bringeth them to their desired haven.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
O let them praise the LORD for his goodness. For his wonderful works to the children of men!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Let them extol him in the congregation of the people, And praise him in the assembly of the elders!
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turneth rivers into a desert, And springs of water into dry ground;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
A fruitful land into barrenness, For the wickedness of them that dwell therein.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He turneth the desert into a lake of water, And dry ground into springs of water;
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And there he causeth the hungry to dwell, And they build a city for a dwelling-place,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And sow fields and plant vineyards, Which yield a fruitful increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
He blesseth them, so that they multiply greatly, And suffereth not their cattle to decrease.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
When they are diminished and brought low By oppression, affliction, and sorrow,
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He poureth contempt upon princes, And causeth them to wander in a pathless wilderness;
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
But he raiseth the poor from their affliction, And increaseth their families like a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The righteous see it and rejoice, And all iniquity shutteth her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Whoso is wise, let him observe this, And have regard to the loving-kindness of the LORD!