< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
“Give thanks to YHWH, For [He is] good, for His kindness [is] for all time”:
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let the redeemed of YHWH say [so], Whom He redeemed from the hand of an adversary.
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
And has gathered them from the lands, From east and from west, From north, and from the sea.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They wandered in a wilderness, in a desert by the way, They have not found a city of habitation.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hungry—indeed—thirsty, Their soul becomes feeble in them,
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
And they cry to YHWH in their adversity, He delivers them from their distress,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
And causes them to tread in a right way, To go to a city of habitation.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For He has satisfied a longing soul, And has filled a hungry soul [with] goodness.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Inhabitants of dark places and death-shade, Prisoners of affliction and of iron,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Because they changed the saying of God, And despised the counsel of the Most High.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
And He humbles their heart with labor, They have been feeble, and there is no helper.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
And they cry to YHWH in their adversity, He saves them from their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brings them out from the dark place, And death-shade, And He draws away their bands.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For He has broken doors of bronze, And He has cut bars of iron.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Fools, by means of their transgression, And by their iniquities, afflict themselves.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soul detests all food, And they come near to the gates of death,
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
And cry to YHWH in their adversity, He saves them from their distresses,
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sends His word and heals them, And delivers [them] from their destructions.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men,
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
And they sacrifice sacrifices of thanksgiving, And recount His works with singing.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Those going down [to] the sea in ships, Doing business in many waters,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
They have seen the works of YHWH, And His wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
And He commands, and appoints a storm, And it lifts up its billows,
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They go up [to] the heavens, they go down [to] the depths, Their soul is melted in evil.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They reel to and fro, and move as a drunkard, And all their wisdom is swallowed up.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
And they cry to YHWH in their adversity, And He brings them out from their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He calms a whirlwind, And their billows are hushed.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
And they rejoice because they are quiet, And He leads them to the haven of their desire.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
They confess to YHWH His kindness, And His wonders to the sons of men,
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
And they exalt Him in [the] assembly of [the] people, And praise Him in [the] seat of [the] elderly.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He makes rivers become a wilderness, And fountains of waters become dry land.
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
A fruitful land becomes a barren place, For the wickedness of its inhabitants.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He makes a wilderness become a pool of water, And a dry land become fountains of waters.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And He causes the hungry to dwell there, And they prepare a city of habitation.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And they sow fields, and plant vineyards, And they make fruits of increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
And He blesses them, and they multiply exceedingly, And He does not diminish their livestock.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
And they are diminished, and bow down, By restraint, evil, and sorrow.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He is pouring contempt on nobles, And causes them to wander in vacancy—no way.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
And sets the needy on high from affliction, And places families as a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The upright see and rejoice, And all perversity has shut her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Who [is] wise, and observes these? They understand the kind acts of YHWH!