< Zabura 107 >
1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Praise the Lord, because he is good: for his mercie endureth for euer.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let them, which haue bene redeemed of the Lord, shewe how he hath deliuered them from the hand of the oppressour,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
And gathered them out of the lands, from the East and from the West, from the North and from the South.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
When they wandered in the desert and wildernesse out of the waie, and founde no citie to dwell in,
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Both hungrie and thirstie, their soule fainted in them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried vnto the Lord in their trouble, and he deliuered them from their distresse,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
And led them forth by the right way, that they might goe to a citie of habitation.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them therefore confesse before ye Lord his louing kindnesse, and his wonderfull woorkes before the sonnes of men.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfied the thirstie soule, and filled the hungrie soule with goodnesse.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
They that dwell in darkenesse and in the shadowe of death, being bounde in miserie and yron,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Because they rebelled against the wordes of the Lord, and despised the counsell of the most High,
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
When he humbled their heart with heauines, then they fell downe and there was no helper.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried vnto the Lord in their trouble, and he deliuered them from their distresse.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brought them out of darkenes, and out of the shadowe of death, and brake their bandes asunder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them therefore cofesse before the Lord his louing kindnesse, and his wonderfull woorkes before the sonnes of men.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For hee hath broken the gates of brasse, and brast the barres of yron asunder.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Fooles by reason of their transgression, and because of their iniquities are afflicted.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soule abhorreth al meat, and they are brought to deaths doore.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they crie vnto the Lord in their trouble, and he deliuereth them from their distresse.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sendeth his worde and healeth them, and deliuereth them from their graues.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them therefore cofesse before the Lord his louing kindnesse, and his wonderful workes before the sonnes of men,
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
And let them offer sacrifices of praise, and declare his workes with reioycing.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
They that goe downe to the sea in ships, and occupie by the great waters,
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
They see the woorkes of the Lord, and his wonders in the deepe.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
For he commaundeth and raiseth the stormie winde, and it lifteth vp the waues thereof.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They mount vp to the heauen, and descend to ye deepe, so that their soule melteth for trouble.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They are tossed to and from, and stagger like a drunken man, and all their cunning is gone.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they crie vnto the Lord in their trouble, and he bringeth them out of their distresse.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He turneth the storme to calme, so that the waues thereof are still.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
When they are quieted, they are glad, and hee bringeth them vnto the hauen, where they would be.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them therfore confesse before the Lord his louing kindnesse, and his wonderfull woorkes before the sonnes of men.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
And let them exalt him in the Congregation of the people, and praise him in the assembly of the Elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turneth the floodes into a wildernesse, and the springs of waters into drinesse,
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
And a fruitfull land into barrennes for the wickednes of them that dwell therein.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Againe hee turneth the wildernesse into pooles of water, and the drie lande into water springs.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And there he placeth the hungrie, and they builde a citie to dwell in,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And sowe the fieldes, and plant vineyardes, which bring foorth fruitfull increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
For he blesseth them, and they multiplie exceedingly, and he diminisheth not their cattell.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Againe men are diminished, and brought lowe by oppression, euill and sorowe.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He powreth contempt vpon princes, and causeth them to erre in desert places out of the way.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Yet he raiseth vp the poore out of miserie, and maketh him families like a flocke of sheepe.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The righteous shall see it, and reioyce, and all iniquitie shall stoppe her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Who is wise that hee may obserue these things? for they shall vnderstand the louing kindnesse of the Lord.