< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alleluia. Give thanks to the Lord, for he is good; for his mercy [endures] for ever.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let them say [so] who have been redeemed by the Lord, whom he has redeemed from the hand of the enemy;
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
and gathered them out of the countries, from the east, and west, and north, and south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They wandered in the wilderness in a dry land; they found no way to a city of habitation.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hungry and thirsty, their soul fainted in them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their affliction, and he delivered them out of their distresses.
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
And he guided them into a straight path, that they might go to a city of habitation.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them acknowledge to the Lord his mercies, and his wonderful works to the children of men.
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfies the empty soul, and fills the hungry [soul] with good things,
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
[even] them that sit in darkness and the shadow of death, fettered in poverty and iron;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
because they rebelled against the words of God, and provoked the counsel of the Most High.
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
So their heart was brought low with troubles; they were weak, and there was no helper.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their affliction, and he saved them out of their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
And he brought them out of darkness and the shadow of death, and broke their bonds asunder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Let them acknowledge to the Lord his mercies, and his wonders to the children of men.
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he broke to pieces the brazen gates, and crushed the iron bars.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
He helped them out of the way of their iniquity; for they were brought low because of their iniquities.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soul abhorred all meat; and they drew near to the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried to the Lord in their affliction, and he saved them out of their distresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sent his word, and healed them, and delivered them out of their destructions.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them acknowledge to the Lord his mercies, and his wonderful works to the children of men.
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
And let them offer to him the sacrifice of praise, and proclaim this works with exultation.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
They that go down to the sea in ships, doing business in many waters;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
these [men] have seen the works of the Lord, and his wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
He speaks, and the stormy wind arises, and its waves are lifted up.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They go up to the heavens, and go down to the depths; their soul melts because of troubles.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They are troubled, they stagger as a drunkard, and all their wisdom is swallowed up.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cry to the Lord in their affliction, and he brings them out of their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
And he commands the storm, and it is calmed into a gentle breeze, and its waves are still.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
And they are glad, because they are quiet; and he guides them to their desire haven.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Let them acknowledge to the Lord his mercies, and his wonderful works to the children of men.
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Let them exalt him in the congregation of the people, and praise him in the seat of the elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turns rivers into a desert, and streams of water into a dry land;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
a fruitful land into saltness, for the wickedness of them that dwell in it.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He turns a wilderness into pools of water, and a dry land into streams of water.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And there he causes the hungry to dwell, and they establish for themselves cities of habitation.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And they sow fields, and plant vineyards, and they yield fruit of increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
And he blesses them, and they multiply exceedingly, and he diminishes not the number of their cattle.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Again they become few, and are brought low, by the pressure of evils and pain.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Contempt is poured upon their princes, and he causes them to wander in a desert and trackless land.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
But he helps the poor out of poverty, and makes [him] families as a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The upright shall see and rejoice; and all iniquity shall stop her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Who is wise, and will observe these things, and understand the mercies of the Lord?

< Zabura 107 >