< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
O give thanks unto Jehovah; for he is good; For his lovingkindness [endureth] for ever.
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Let the redeemed of Jehovah say [so], Whom he hath redeemed from the hand of the adversary,
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
And gathered out of the lands, From the east and from the west, From the north and from the south.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
They wandered in the wilderness in a desert way; They found no city of habitation.
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Hungry and thirsty, Their soul fainted in them.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Then they cried unto Jehovah in their trouble, And he delivered them out of their distresses,
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
He led them also by a straight way, That they might go to a city of habitation.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Oh that men would praise Jehovah for his lovingkindness, And for his wonderful works to the children of men!
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
For he satisfieth the longing soul, And the hungry soul he filleth with good.
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Such as sat in darkness and in the shadow of death, Being bound in affliction and iron,
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Because they rebelled against the words of God, And contemned the counsel of the Most High:
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Therefore he brought down their heart with labor; They fell down, and there was none to help.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cried unto Jehovah in their trouble, And he saved them out of their distresses.
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
He brought them out of darkness and the shadow of death, And brake their bonds in sunder.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Oh that men would praise Jehovah for his lovingkindness, And for his wonderful works to the children of men!
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
For he hath broken the gates of brass, And cut the bars of iron in sunder.
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Fools because of their transgression, And because of their iniquities, are afflicted.
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Their soul abhorreth all manner of food; And they draw near unto the gates of death.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Then they cry unto Jehovah in their trouble, And he saveth them out of their distresses.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
He sendeth his word, and healeth them, And delivereth [them] from their destructions.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Oh that men would praise Jehovah for his lovingkindness, And for his wonderful works to the children of men!
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
And let them offer the sacrifices of thanksgiving, And declare his works with singing.
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
They that go down to the sea in ships, That do business in great waters;
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
These see the works of Jehovah, And his wonders in the deep.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
For he commandeth, and raiseth the stormy wind, Which lifteth up the waves thereof.
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
They mount up to the heavens, they go down again to the depths: Their soul melteth away because of trouble.
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
They reel to and fro, and stagger like a drunken man, And are at their wits’ end.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Then they cry unto Jehovah in their trouble, And he bringeth them out of their distresses.
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
He maketh the storm a calm, So that the waves thereof are still.
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Then are they glad because they are quiet; So he bringeth them unto their desired haven.
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Oh that men would praise Jehovah for his lovingkindness, And for his wonderful works to the children of men!
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Let them exalt him also in the assembly of the people, And praise him in the seat of the elders.
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
He turneth rivers into a wilderness, And watersprings into a thirsty ground;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
A fruitful land into a salt desert, For the wickedness of them that dwell therein.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
He turneth a wilderness into a pool of water, And a dry land into watersprings.
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
And there he maketh the hungry to dwell, That they may prepare a city of habitation,
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
And sow fields, and plant vineyards, And get them fruits of increase.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
He blesseth them also, so that they are multiplied greatly; And he suffereth not their cattle to decrease.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
Again, they are diminished and bowed down Through oppression, trouble, and sorrow.
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
He poureth contempt upon princes, And causeth them to wander in the waste, where there is no way.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Yet setteth he the needy on high from affliction, And maketh [him] families like a flock.
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
The upright shall see it, and be glad; And all iniquity shall stop her mouth.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Whoso is wise will give heed to these things; And they will consider the lovingkindnesses of Jehovah.

< Zabura 107 >