< Zabura 107 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Brengt Jahweh dank, want Hij is goed, En zijn genade duurt eeuwig!
2 Bari fansassu na Ubangiji su faɗa wannan, su da aka fansa daga hannun maƙiyi,
Zo moeten getuigen, die door Jahweh verlost zijn, En door Hem uit de nood zijn gered;
3 su da ya tattara daga ƙasashe, daga gabas da yamma, daga arewa da kudu.
Die Hij van alle kant hierheen heeft gebracht, Van oost en west, van noord en zuid.
4 Waɗansu sun yi ta yawo a jejin hamada, ba su sami hanya zuwa birnin da za su zauna ba.
Sommigen doolden in woestijn en wildernis rond, Zonder de weg naar hun woonplaats te vinden;
5 Sun ji yunwa da ƙishirwa, suka kuma fid da zuciya.
Ze leden honger en dorst, En hun leven verkwijnde.
6 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuma cece su daga damuwarsu.
Maar ze riepen Jahweh aan in hun nood, En Hij verloste hen van hun angsten:
7 Ya bishe su ta miƙaƙƙiyar hanya zuwa birnin da za su zauna.
Hij bracht ze weer op de veilige weg, Zodat ze hun woonplaats bereikten.
8 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Laat ze Jahweh voor zijn goedheid dan danken, En voor zijn wonderen voor de kinderen der mensen:
9 gama yana shayar da masu ƙishirwa yana kuma ƙosar da mayunwata da abubuwa masu kyau.
Want den dorstige heeft Hij gelaafd, Den hongerige heeft Hij verzadigd!
10 Waɗansu sun zauna a cikin duhu da kuma zurfin ɓacin rai,’yan kurkuku suna wahala cikin sarƙoƙin ƙarfe,
Anderen zaten in duister en donker, In ellende en boeien gekluisterd;
11 gama sun yi tayarwa a kan maganar Allah suka ƙi shawarar Mafi Ɗaukaka.
Want ze hadden zich tegen Gods geboden verzet, En de vermaning van den Allerhoogste veracht;
12 Saboda haka ya ba da su ga aiki mai wuya; suka yi tuntuɓe, kuma ba mai taimako.
Zo was door rampspoed de moed hun ontzonken, En reddeloos stortten ze neer.
13 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Maar ze riepen Jahweh aan in hun nood, En Hij verloste hen van hun angsten:
14 Ya fitar da su daga duhu da zurfin ɓaci rai ya tsintsinke sarƙoƙinsu.
Hij haalde ze uit het duister en donker, En verbrak hun boeien.
15 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane,
Laat ze Jahweh voor zijn goedheid dan danken, En voor zijn wonderen voor de kinderen der mensen:
16 gama ya farfashe ƙofofin tagulla ya kuma ragargaza ƙyamaren ƙarfe.
Want metalen poorten heeft Hij verbrijzeld, Ijzeren grendels in stukken geslagen!
17 Waɗansu suka zama wawaye ta wurin hanyoyinsu na tayarwa suka kuwa sha wahala saboda laifofinsu.
Anderen werden ziek door hun zondige wandel, Hadden smarten te lijden om hun schuld;
18 Ba su so su ga abinci ba suka kuwa kai bakin mutuwa.
Alle voedsel begon hun te walgen, En ze stonden al dicht bij de poorten des doods.
19 Sa’an nan suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa cece su daga damuwarsu.
Maar ze riepen Jahweh aan in hun nood, En Hij verloste hen van hun angsten.
20 Ya ba da umarninsa ya kuma warkar da su ya kuɓutar da su daga kabari.
Hij sprak: en ze werden genezen, En Hij ontrukte hen weer aan het graf.
21 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Laat ze Jahweh voor zijn goedheid dan danken, En voor zijn wonderen voor de kinderen der mensen:
22 Bari su miƙa hadaya ta godiya su kuma ba da labarin ayyukansa da waƙoƙin farin ciki.
Laat ze dankoffers brengen, En jubelend zijn werken vermelden!
23 Waɗansu suka yi tafiya a teku cikin jiragen ruwa; su’yan kasuwa ne a manyan ruwaye.
Anderen staken op schepen in zee, Om handel te drijven op de onmetelijke wateren.
24 Sun ga ayyukan Ubangiji, ayyukansa masu banmamaki a cikin zurfin teku.
Ook zij hebben Jahweh’s werken aanschouwd, In de kolken zijn wonderen.
25 Gama ya yi magana ya kuma sa iska mai ƙarfi ta tashi ya ɗaga raƙuman ruwa sama.
Hij sprak: en er stak een stormwind op, Die zwiepte de golven omhoog;
26 Suka hau zuwa sammai suka kuma tsinduma cikin zurfafa; a cikin azabarsu sai ƙarfin halinsu ya karai.
Ze vlogen op naar de hemel, ploften neer in de diepten, En vergingen van angst;
27 Suka yi tangaɗi suna tuntuɓe kamar bugaggu; suka kuma kai ga ƙarshen dabararsu.
Ze rolden en tuimelden, als waren ze dronken, En al hun zeemanschap was tevergeefs.
28 Sai suka yi kuka ga Ubangiji cikin wahalarsu, ya kuwa fitar da su daga damuwarsu.
Maar ze riepen Jahweh aan in hun nood, En Hij verloste hen van hun angsten:
29 Ya kwantar da hadiri suka yi tsit; raƙuman ruwan teku suka yi shiru.
Hij bedaarde de storm tot een bries, En de golven legden zich neer;
30 Suka yi murna sa’ad da wuri ya kwanta, ya kuma bishe su zuwa inda suka so su kai.
Wat waren ze blij, toen het kalm was geworden, En Hij hen naar de verbeide haven geleidde!
31 Bari su yi godiya ga Ubangiji saboda ƙaunarsa marar ƙarewa da kuma ayyukansa masu banmamaki saboda mutane.
Laat ze Jahweh voor zijn goedheid dan danken, En voor zijn wonderen voor de kinderen der mensen:
32 Bari su ɗaukaka shi cikin taron mutane su kuma yabe shi cikin taron dattawa.
Hem in de volksgemeente roemen, Hem in de raad der oudsten prijzen!
33 Ya mai da koguna suka zama hamada, maɓulɓulai masu gudu suka zama ƙasa mai ƙishirwa,
Rivieren maakt Hij tot steppe, Waterbronnen tot dorstige grond;
34 ƙasa mai amfani kuma suka zama gishiri marar amfani, saboda muguntar waɗanda suka zauna a can.
Vruchtbaar land tot zilte bodem, Om de boosheid van zijn bewoners.
35 Ya mai da hamada ya zama tafkunan ruwa busasshiyar ƙasa kuma zuwa maɓulɓulai masu gudu;
Maar van de steppe maakt Hij een vijver, Waterbronnen van het dorre land;
36 a can ya kai mayunwata su yi zama, ya kuma samo birnin da za su zauna.
Daar zet Hij de hongerigen neer, Om er zich een woonplaats te stichten.
37 Suka yi shuka a gonaki suka dasa inabi suka kuma girbe amfani gona;
Ze bezaaien hun akkers, beplanten hun gaarden, En oogsten hun vruchten.
38 ya albarkace su, yawansu kuma ya ƙaru, bai kuwa bar garkunansu suka ragu ba.
Hij zegent hen: ze worden zeer talrijk, En Hij vermeerdert hun vee.
39 Sa’an nan yawansu ya ragu, aka kuma ƙasƙantar da su ta wurin danniya, bala’i da kuma baƙin ciki;
En nemen ze af in getal, en gaan ze ten onder Door verdrukking, ellende en jammer:
40 shi da yake kawo reni a kan manyan mutane ya sa suka yi ta yawo a cikin jejin da ba hanya.
Dan geeft Hij de tyrannen prijs aan de schande, En laat ze door de wildernis dolen.
41 Amma ya fid da mabukata daga wahalarsu ya kuma ƙara iyalansu da tumakinsu.
Maar den arme heft Hij uit de ellende weer op, En maakt zijn geslacht weer talrijk als kudden:
42 Masu yin gaskiya suka gani suka yi farin ciki amma dukan mugaye suka rufe bakunansu.
De vromen zien het, en juichen; Maar wat boos is, zwijgt stil.
43 Duk mai hikima, bari yă ji waɗannan abubuwa yă kuma lura da ƙauna mai girma ta Ubangiji.
Wie wijs is, neemt het ter harte, En beseft de goedheid van Jahweh!

< Zabura 107 >