< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Msifuni Yahwe. Mshukuruni Yahwe, kwa kuwa ni mwema, kwa maana uaminifu wa agano lake wadumu milele.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Ni nani awezaye kuyahesabu mataendo makuu ya yahwe au kutangaza katika ukamilifu sifa zote za matendo yake ya kuaminika.
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Wamebarikiwa wale watendao yaliyo mema na matendo yao yaliyo haki siku zote.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Ukumbuke, Ee Yahwe, unapowaonesha watu wako neema; unisaidie unapowaokoa.
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Ndipo nitaona mafanikio ya wateule wako, wakifurahia katika furaha ya taifa lako, na utukufu pamoja na urithi wako.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Tumefanya dhambi kama babu zetu, tumekosea, na kufanya uovu.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Baba zetu hawakuyatambua matendo yako ya ajabu katika Misri; walipuuzia matendo yako mengi ya uaminifu wa agano; waliasi penye bahari, bahari ya Shamu.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Hata hivyo, yeye aliwaokoa kwa ajili ya jina lake ili kwamba aweze kuzifunua nguvu zake.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Aliikemea Bahari ya Shamu, nayo ikakauka. Kisha akawaongoza vilindini, kana kwamba ni jangwani.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Aliwaokoa kutoka mkononi mwa wale waliowachukia, na aliwaokoa kutoka mkononi mwa adui.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Lakini maji yaliwafunika washindani wao; hakuna hata mmoja aliye okolewa.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Ndipo waliyaamini maneno yake, nao waliimba sifa zake.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Lakini walisahau haraka kile alichofanya; hawakuyasubiri maelekezo yake.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Walikuwa na tamaa isiyotoshelezwa jangwani, wakamjaribu Mungu nyikani.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Aliwapa ombi lao, lakini alituma gonjwa ambalo lilishambulia miili yao.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Katika kambi wakawa na wivu juu Musa na Haruni, kuhani mtakatifu wa Yahwe.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Nchi ilifunguka na ilimmeza Dathani na iliwafunika wafuasi wa Abiramu.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Moto uliwaka kati yao; moto uliwaangamiza waovu.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Walitengeneza ndama huko Horebu na kuabudu sanamu ya kuyeyuka.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Wakaubadili utukufu wa Mungu kuwa mfano wa ng'ombe alaye majani.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Walimsahau Mungu wokozi wao, aliyefanya mambo makuu katika Misri.
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Alifanya matendo ya ajabu katika nchi ya Hamu na matendo makuu penye Bahari ya Shamu.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Mungu angetangaza uharibifu wao, kama sio Musa, mteule wake, aliingilia kati kugeuza hasira yake dhidi ya kuwaangamiza.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Kisha waliidharau nchi yenye matunda; hawakuiamini ahadi yake,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
bali walilalamiaka katika mahema yao, na hawakumtii Yahwe.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Kwa hiyo aliinua mkono wake na kuapa kwao kuwa atawaacha wafe jangwani,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
akitawanya uzao wao kati ya mataifa, na kuwatawanya katika nchi za kigeni.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Waliabudu Baal ya Poeri na walizila dhabihu zilizotolewa kwa wafu.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Walimkasirisha kwa matendo yao, na pigo la gonjwa baya liliwashambulia kati yao.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Ndipo Finehasi aliinuka kuingilia kati, na pigo likakoma.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Ilihesabika kwake kama tendo la haki kwa vizazi vyote hata milele.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Pia walimkasirisha Yahwe penye maji ya Meriba, na Musa aliteseka kwa ajili yao.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Walimghadhabisha Musa naye akaongea haraka.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Hawakuyaharibu mataifa kama Yahwe alivyowaamuru,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
bali walichangamana na mataifa na walijifunza njia zao
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
nao waliabudu sanamu, nazo zikawa mtego kwao.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Waliwatoa wana wao na binti zao kwa mapepo.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Walimwaga damu isiyo na hatia, damu ya wana na binti zao, ambao waliwatoa kama dhabihu kwa sanamu za Kanaani, waliinajisi nchi kwa damu.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Walinajisiwa kwa matendo yao; katika matendo yao walikuwa kama malaya.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Hivyo Yahwe aliwakasilikia watu wake, akawadharau watu wake mwenyewe.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Akawaruhusu mataifa, na wale walio wachukia wakawatawala.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Maadui zao wakawaonea, wakatiishwa chini ya mamlaka yao.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Mara nyingi alienda kuwasaidia, lakini waliendelea kuasi nao walishushwa chini kwa dhambi zao wenyewe.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Hata hivyo, aliiangalia dhiki yao aliposikia kilio chao kwa ajili ya msaada.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Alikumbuka agano lake pamoja nao na alijirudi kwa sababu ya upendo wake thabiti.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Aliwafanya wote waliowateka wawahurumie.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Utuokoe, Ee Yahwe, Mungu wetu. Utukusanye kutoka kati ya mataifa ili kwamba tuweze kulishukuru jina lako takatifu na utukufu katika sifa zako. Yahwe,
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Mungu wa Israeli, na asifiwe toka milele na milele. watu wote walisema, “Amen.” Msifuni Yahwe. Kitabu cha tano.

< Zabura 106 >