< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Dejen que el Señor sea alabado. Alaben al Señor, porque él es bueno; porque su misericordia es inmutable para siempre.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
¿Quién puede dar cuenta de los grandes actos del Señor, o dejar en claro toda su alabanza?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Felices son aquellos cuyas decisiones son rectas, y el que hace justicia todo el tiempo.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Recuerda, oh Señor, cuando eres bueno con tu pueblo; Oh, deja que tu salvación venga a mí;
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Para que pueda ver el bienestar de las personas de tu elección y participe en la alegría de tu nación y enorgullezca de tu herencia.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Somos pecadores como nuestros padres, hemos hecho mal, nuestros actos son malos.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nuestros padres no pensaron en tus maravillas en Egipto; ellos no guardaron en la memoria la gran cantidad de tus misericordias, sino que te dieron motivos para la ira en el mar, incluso en el Mar Rojo.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Pero él era su salvador a causa de su nombre, para que los hombres pudieran ver su gran poder.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Por su palabra, el mar Rojo se secó, y él los llevó por las aguas profundas como a través del desierto.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Y los tomó a salvo de las manos de sus enemigos, y los mantuvo lejos de los ataques de los que estaban contra ellos.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Y las aguas pasaron sobre sus enemigos; todos ellos llegaron a su fin.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Entonces tuvieron fe en su palabra; ellos le dieron canciones de alabanza.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Pero el recuerdo de sus obras fue breve; no esperando ser guiado por él,
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Ellos dieron paso a sus malos deseos en la tierra baldía, y pusieron a Dios a prueba en el desierto.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Y él les dio su pedido, pero envió una enfermedad devastadora en sus almas.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Estaban llenos de envidia contra Moisés en las tiendas, y contra Aarón, el santo del Señor.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
La apertura de la tierra puso fin a Datán, cubriendo a Abiram y su banda.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Y se encendió un fuego entre sus tiendas; los pecadores fueron quemados por las llamas.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Hicieron un becerro en Horeb, y adoraron a una imagen de oro.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Y su gloria fue transformada en imagen de buey, cuyo alimento es hierba.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
No tenían memoria de Dios su salvador, que había hecho grandes cosas en Egipto;
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Obras de maravilla en la tierra de Ham, y cosas de miedo en el Mar Rojo.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Y él se proponía poner fin a ellos si Moisés, su siervo especial, no se hubiera levantado delante de él, entre él y su pueblo, haciendo retroceder su ira, para guardarlos de la destrucción.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Estaban disgustados con la buena tierra; no tenían fe en su palabra;
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Hablando contra él secretamente en sus tiendas, no escucharon la voz del Señor.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Entonces les juró que los exterminaría en la tierra baldía.
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
para que sus hijos se mezclen entre las naciones, y sean enviados a otras tierras.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Y se juntaron con Baal-peor, y tomaron parte en las ofrendas a los muertos.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Entonces lo enojaron por su comportamiento; y él envió enfermedad sobre ellos.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Entonces se levantó Finees y oró por ellos; y la enfermedad no se expandió.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Y todas las generaciones que vinieron después de él guardaban para siempre el recuerdo de su justicia.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
E hicieron enojar a Dios otra vez en las aguas de Meriba, y Moisés se angustió por causa de ellos;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Porque ellos hicieron amargar su espíritu, y él dijo cosas impías.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
No pusieron fin a los pueblos, como el Señor había dicho;
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Pero se unieron a las naciones, aprendiendo sus obras.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Y adoraron a las imágenes; que eran un peligro para ellos:
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Incluso hicieron ofrendas de sus hijos y sus hijas a espíritus malignos,
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Y dieron la sangre de sus hijos y de sus hijas que no habían hecho mal, ofreciéndolas a las imágenes de Canaán; y la tierra quedó contaminada con sangre.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Y se contaminaron con sus obras, yendo tras sus malos deseos.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Entonces la ira del Señor ardió contra su pueblo, y él se enojó contra su heredad.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Y él los entregó en manos de las naciones; y fueron gobernados por sus enemigos.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Por ellos fueron aplastados, y humillados bajo sus manos.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Una y otra vez los hizo libres; pero sus corazones se volvieron contra su propósito, y fueron vencidos por sus pecados.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Pero cuando su clamor llegó a sus oídos, tuvo piedad de su problema:
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Y tuvo en cuenta su acuerdo con ellos, y en su gran misericordia les dio el perdón.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Él puso lástima en los corazones de aquellos que los hicieron prisioneros.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Sé nuestro Salvador, Señor Dios nuestro, y nos volvamos a reunir de entre las naciones, para que glorifiquemos tu santo nombre y nos gloriamos en tu alabanza.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Alabado sea el Señor Dios de Israel por los siglos de los siglos; y que toda la gente diga: que así sea. Alaba al Señor.