< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
¡Aleluya! Den gracias a Yavé, Porque Él es bueno, Porque para siempre es su misericordia.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
¿Quién puede contar las proezas de Yavé? ¿Quién proclama toda su alabanza?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
¡Dichosos los que guardan recto juicio, Los que practican justicia en todo tiempo!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Acuérdate de mí, oh Yavé, Según tu buena voluntad para tu pueblo. Visítame con tu salvación,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Para que yo vea el bien de tus escogidos, Para que me regocije por la alegría de tu pueblo, Que me gloríe con tu heredad.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Como nuestros antepasados pecamos. Cometimos iniquidad. Nos portamos perversamente.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nuestros antepasados no entendieron tus maravillas en Egipto. No recordaron tus numerosas bondades, Sino se rebelaron junto al mar, en el mar Rojo.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Pero Él los salvó por amor a su Nombre Para que fuera evidente su poder.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Reprendió al mar Rojo Y lo secó, Y los condujo por las profundidades, Como por un desierto.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Así los salvó de [la] mano del que [los] odiaba, Y los redimió de la mano del enemigo.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Cubrieron las aguas a sus adversarios, No quedó ni uno de ellos.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Entonces creyeron a sus Palabras, Y cantaron su alabanza.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Muy pronto olvidaron sus obras. No esperaron su consejo.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Con avidez desearon comer en el desierto, Y en lugar despoblado tentaron a ʼElohim.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Él les dio lo que pidieron, Pero envió mortandad sobre ellos.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Tuvieron envidia de Moisés en el campamento, Y de Aarón, el consagrado a Yavé.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Se abrió la tierra Y se tragó a Datán, Y cubrió al grupo de Abiram.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Un fuego se encendió contra su grupo. La llama devoró a los perversos.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Hicieron un becerro en Horeb. Se postraron ante una imagen de fundición.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Así cambiaron la Gloria de ellos Por la imagen de un becerro que come hierba.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Olvidaron al ʼEL, su Salvador, Quien hizo grandes cosas en Egipto,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Maravillas en la tierra de Cam, Portentos en el mar Rojo.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Por tanto Él dijo que los destruiría. Si no fuera porque Moisés su escogido, Se puso en la brecha delante de Él Con la intención de que no los destruyera.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Luego despreciaron [la] tierra deseable. No creyeron en la Palabra de Él,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Sino murmuraron en sus tiendas. No escucharon la voz de Yavé.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Por tanto les juró Que caerían en el desierto,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Que dispersaría su descendencia entre las naciones Y los esparciría por las tierras.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Se unieron también a Baal-peor Y comieron lo sacrificado a los muertos.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Así [lo] provocaron a ira con sus obras, Y una mortandad irrumpió entre ellos.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Pero Finees se levantó e intervino, Y la mortandad se detuvo,
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Y le fue atribuido como justicia Por todas las generaciones para siempre.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
También [lo] provocaron a ira en las aguas de Meriba, Y salió mal Moisés por causa de ellos,
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Porque hicieron rebelar su espíritu, Y él habló precipitadamente con sus labios.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
No destruyeron a los pueblos, Como Yavé les mandó,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Sino se mezclaron con gentiles. Aprendieron sus prácticas,
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Y sirvieron a sus ídolos, Los cuales fueron una trampa.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Sacrificaron sus hijos y sus hijas a los demonios
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Y derramaron sangre inocente, La sangre de sus hijos y de sus hijas, A quienes sacrificaron a los ídolos de Canaán, Y la tierra fue contaminada con la sangre.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Así se contaminaron con las prácticas de ellos, Y se prostituyeron con sus hechos.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Por tanto la ira de Yavé se encendió contra su pueblo, Y Él repugnó su heredad.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Los entregó en [la] mano de los gentiles, Y aquellos que los odiaban gobernaron sobre ellos.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Sus enemigos también los oprimieron, Y fueron sometidos bajo su poder.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Muchas veces los libró, Pero ellos se rebelaron contra su consejo en su designio, Y así se hundieron en su iniquidad.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Sin embargo, Él miraba su angustia Y escuchaba su clamor.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Recordaba su Pacto por amor a ellos, Y se compadecía según la grandeza de su misericordia.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
También promovió que fueran [objeto] de misericordia Por parte de todos los que los tenían cautivos.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Oh Yavé, ʼElohim nuestro, sálvanos. Recógenos de entre las naciones, Para que demos gracias a tu santo Nombre Y nos gloriemos en tus alabanzas.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
¡Bendito sea Yavé, el ʼElohim de Israel, Desde la eternidad hasta la eternidad! Y todo el pueblo diga: ¡Amén! ¡Aleluya!