< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
¡Alabado sea Yahvé! Dad gracias a Yahvé, porque es bueno, porque su bondad es eterna.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
¿Quién puede pronunciar los actos poderosos de Yahvé? o declarar plenamente todas sus alabanzas?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Dichosos los que guardan la justicia. Dichoso el que hace lo correcto en todo momento.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Acuérdate de mí, Yahvé, con el favor que muestras a tu pueblo. Visítame con tu salvación,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
para que vea la prosperidad de tus elegidos, para que me regocije en la alegría de tu nación, para que me gloríe con tu herencia.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Hemos pecado con nuestros padres. Hemos cometido una iniquidad. Hemos hecho maldades.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nuestros padres no entendieron tus maravillas en Egipto. No recordaron la multitud de tus bondades amorosas, pero fueron rebeldes en el mar, incluso en el Mar Rojo.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Sin embargo, los salvó por su nombre, para dar a conocer su poderoso poder.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
También reprendió al Mar Rojo, y se secó; por lo que los condujo a través de las profundidades, como a través de un desierto.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Los salvó de la mano del que los odiaba, y los redujo de la mano del enemigo.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Las aguas cubrieron a sus adversarios. No quedaba ni uno de ellos.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Entonces creyeron en sus palabras. Cantaron sus alabanzas.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Pronto olvidaron sus obras. No esperaron su consejo,
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
pero cedió al deseo en el desierto, y puso a prueba a Dios en el páramo.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Les concedió su petición, sino que enviaron a su alma la delgadez.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
También envidiaban a Moisés en el campamento, y Aarón, el santo de Yahvé.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
La tierra se abrió y se tragó a Datán, y cubrió la compañía de Abiram.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Se encendió un fuego en su compañía. La llama quemó a los malvados.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Hicieron un becerro en Horeb, y adoraron una imagen fundida.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Así intercambiaron su gloria para una imagen de un toro que come hierba.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Se olvidaron de Dios, su Salvador, que había hecho grandes cosas en Egipto,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
obras maravillosas en la tierra de Cam, y cosas impresionantes junto al Mar Rojo.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Por eso dijo que los destruiría, si Moisés, su elegido, no se hubiera puesto delante de él en la brecha, para alejar su ira, para que no los destruya.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Sí, despreciaron la tierra agradable. No creyeron en su palabra,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
sino que murmuraban en sus tiendas, y no escucharon la voz de Yahvé.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Por eso les juró que los derrocaría en el desierto,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
que él derrocaría a su descendencia entre las naciones, y dispersarlos en las tierras.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
También se unieron a Baal Peor, y comieron los sacrificios de los muertos.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Así le provocaron la ira con sus actos. La peste se abatió sobre ellos.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Entonces Finees se levantó y ejecutó el juicio, por lo que la plaga fue detenida.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Eso se le acreditó como justicia, para todas las generaciones venideras.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
También lo enfurecieron en las aguas de Meribá, por lo que Moisés se preocupó por ellos;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
porque eran rebeldes a su espíritu, habló precipitadamente con los labios.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
No destruyeron los pueblos, como les ordenó Yahvé,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
sino que se mezclaron con las naciones, y aprendieron sus obras.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Servían a sus ídolos, que se convirtió en una trampa para ellos.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Sí, sacrificaron a sus hijos e hijas a los demonios.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Derramaron sangre inocente, incluso la sangre de sus hijos y de sus hijas, que sacrificaron a los ídolos de Canaán. La tierra estaba contaminada con sangre.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Así se contaminaron con sus obras, y se prostituyeron en sus actos.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Por eso Yahvé ardió de ira contra su pueblo. Aborrecía su herencia.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Los entregó en manos de las naciones. Los que los odiaban los gobernaban.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Sus enemigos también los oprimieron. Fueron sometidos bajo su mano.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Los rescató muchas veces, pero fueron rebeldes en su consejo, y fueron abatidos en su iniquidad.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Sin embargo, él consideró su angustia, cuando escuchó su grito.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Se acordó por ellos de su pacto, y se arrepintió según la multitud de sus bondades.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
También hizo que se compadecieran de ellos por todos aquellos que los llevaron cautivos.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Sálvanos, Yahvé, nuestro Dios, reunirnos de entre las naciones, para dar gracias a tu santo nombre, ¡para triunfar en tu alabanza!
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Bendito sea Yahvé, el Dios de Israel, ¡desde la eternidad hasta la eternidad! Que todo el pueblo diga: “Amén”. ¡Alabado sea Yah!