< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Aleluja! Slavite Gospoda, ker je dober, ker je vekomaj milost njegova.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Kdo bi dopovedal najvišjo moč Gospodovo, oznanil vso hvalo njegovo?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
O blagor jim, ki se držé postave té, ki delajo pravico vsak čas!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Spomni se me, Gospod, po blagovoljnosti, katero izkazuješ svojemu ljudstvu, obišči me z blaginjo svojo.
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Da uživam izvoljenih tvojih dobroto, da se radujem radosti naroda tvojega; da se s posestjo tvojo ponašam.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Grešili smo z očeti svojimi: krivično smo delali, ravnali hudobno.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Očetje naši niso umeli v Egiptu čudovitih dél tvojih; spominjali se niso milosti tvojih obilosti; temuč priliko so dajali izpremeniti jih pri morji, ko so stopali v morje trstovito.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Vendar jih je rešil zavoljo imena svojega, da bi pokazal svojo moč.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Ker zarotil je trstovito morje, in posušilo se je; in peljal jih je skozi valove kakor skozi puščavo.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Tako jih je rešil roke sovražnikove; otel jih je neprijateljeve roke.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Pokrile pa so vode njih sovražnike; eden izmed njih ni ostal.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Da sì so verjeli besedam njegovim, peli hvalo njegovo,
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Pozabili so naglo dél njegovih; čakali niso sveta njegovega.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Ampak iz poželjivosti v puščavi izkušali so Boga mogočnega v samoti.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Tako da je podelivši jim, kar so prosili, poslal kugo nad nje.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Potem ko so bili nevoščljivi Mojzesu v šatorji, Aronu svetniku Gospodovemu,
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Odprla se je zemlja in požrla Datana in zagrnila je drhal Abiramovo.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
In vnel se je ogenj v njih drhal, in s plamenom požgal krivične.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Naredili so tele na Horebu, in klanjali so se podobi.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
In premenivši čast svojo v podobo vola, ki travo jé,
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Pozabili so Boga mogočnega, rešitelja svojega, kateri je bil storil velike reči v Egiptu,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Čudovita dela v deželi Kamovi, strašna pri trstovitem morji.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Zatorej je rekel, da jih bode pogubil; ko bi ne bil Mojzes, izvoljenec njegov, stopil v ón predór pred njim, da bi odvrnil jezo njegovo, da jih ne pogubi.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Zavrgli so tudi zaželeno deželo, ne verujoč besedi njegovi.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
In godrnjaje v šatorih svojih niso poslušali glasú Gospodovega.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Zatorej je dvignil roko svojo ter prisegel, da jih podere v sami puščavi.
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
In da podere seme njih med narodi, in razkropi jih po deželah.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Razen tega so se združili tudi z malikom Peorjem, in jedli mrtvih daritve.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Klicali so tako Boga v nevoljo z deli svojimi, da je pridrla nad nje nadloga.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Dokler ni vstal Pineas in storil sodbo, ter je bila ustavljena tista nadloga;
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Kar se mu je štelo za pravico, od roda do roda vekomaj.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Enako so razdražili gorečo jezo pri vodah prepira, tako da se je slabo godilo Mojzesu zavoljo njih.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Ko so bili razdražili duha njegovega, in je izgovoril z ustnami svojimi razdraženje svoje:
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Pokončali niso onih ljudstev, za katera jim je bil zapovedal Gospod;
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Ampak pomešali so se z onimi narodi in naučili se njih dél.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
In čestili so njih podobe, katere so bile njim v izpotiko.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Ker darovali so sinove svoje in hčere svoje hudobnim duhovom;
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
In prelivali so nedolžno kri, kri sinov svojih in hčer svojih, katere so darovali podobam Kanaanskim, tako da je bila zemlja onečiščena z njih moritvami.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
In oskrunjali so se sè svojimi deli; prešestvovali z dejanji svojimi.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Zatorej se je razsrdil Gospod nad ljudstvom svojim in studil svojo posest,
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Tako da jih je dal v roko narodom, da bi jim gospodovali njih sovražniki, črtilci,
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
In jih zatirali njih neprijatelji, in da bi se poniževali pod njih roko.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Mnogokrat jih je rešil, dasì so ga bili razsrdili z naklepom svojim, in so bili ponižani zavoljo krivice svoje.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Ozrl se je na njih stisko, slišal je njih vpitje.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
In spomnivši se zá nje zaveze svoje, kesal se je po obilosti milosti svojih;
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Tako da jim je izkazal usmiljenje pred vsemí, kateri so jih v sužnjosti imeli.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Reši nas, Gospod, Bog naš, in zberi nas izmed tistih narodov, da slavimo sveto ime tvoje, in se s hvaljenjem priporočamo v hvali tvoji,
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Blagoslovljen Gospod, Izraelov Bog, od veka do veka in vse ljudstvo naj govori: Aleluja!

< Zabura 106 >