< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Исповедайтеся Господеви, яко благ, яко в век милость Его.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Кто возглаголет силы Господни, слышаны сотворит вся хвалы Его?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Блажени хранящии суд и творящии правду во всякое время.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Помяни нас, Господи, во благоволении людий Твоих, посети нас спасением Твоим,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
видети во благости избранныя Твоя, возвеселитися в веселии языка Твоего, хвалитися с достоянием Твоим.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Согрешихом со отцы нашими, беззаконновахом, неправдовахом:
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
отцы наши во Египте не разумеша чудес Твоих, ни помянуша множества милости Твоея: и преогорчиша восходяще в Чермное море.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
И спасе их имене Своего ради, сказати силу Свою:
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
и запрети Чермному морю, и изсяче: и настави я в бездне яко в пустыни.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
И спасе я из руки ненавидящих и избави я из руки врагов.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Покры вода стужающыя им: ни един от них избысть.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
И вероваша словеси Его и воспеша хвалу Его.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Ускориша, забыша дела Его, не стерпеша совета Его:
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
и похотеша желанию в пустыни и искусиша Бога в безводней.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
И даде им прошение их, посла сытость в душы их.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
И прогневаша Моисеа в стану, Аарона святаго Господня.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Отверзеся земля и пожре Дафана и покры на сонмищи Авирона:
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
и разжжеся огнь в сонме их, пламень попали грешники.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
И сотвориша телца в Хориве и поклонишася истуканному:
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
и измениша славу Его в подобие телца ядущаго траву.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
И забыша Бога спасающаго их, сотворшаго велия во Египте,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
чудеса в земли Хамове, страшная в мори Чермнем.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
И рече потребити их, аще не бы Моисей избранный Его стал в сокрушении пред Ним, возвратити ярость Его, да не погубит их.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
И уничижиша землю желанную, не яша веры словеси Его:
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
и поропташа в селениих своих, не услышаша гласа Господня.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
И воздвиже руку Свою на ня, низложити я в пустыни,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
и низложити семя их во языцех, и расточити я в страны.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
И причастишася Веельфегору и снедоша жертвы мертвых:
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
и раздражиша Его в начинаниих своих, и умножися в них падение.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
И ста Финеес и умилостиви, и преста сечь:
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
и вменися ему в правду, в род и род до века.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
И прогневаша Его на воде Пререкания, и озлоблен бысть Моисей их ради:
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
яко преогорчиша дух его и разнствова устнама своима.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Не потребиша языки, яже рече Господь им.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
И смесишася во языцех и навыкоша делом их:
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
и поработаша истуканным их, и бысть им в соблазн.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
И пожроша сыны своя и дщери своя бесовом,
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
и пролияша кровь неповинную, кровь сынов своих и дщерей, яже пожроша истуканным Ханаанским: и убиена бысть земля их кровьми
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
и осквернися в делех их: и соблудиша в начинаниих своих.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
И разгневася яростию Господь на люди Своя и омерзи достояние Свое:
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
и предаде я в руки врагов, и обладаша ими ненавидящии их.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
И стужиша им врази их: и смиришася под руками их.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Множицею избави я: тии же преогорчиша Его советом своим, и смиришася в беззакониих своих.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
И виде Господь, внегда скорбети им, внегда услышаше моление их:
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
и помяну завет Свой, и раскаяся по множеству милости Своея:
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
и даде я в щедроты пред всеми пленившими я.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Спаси ны, Господи, Боже наш, и собери ны от язык, исповедатися имени Твоему святому, хвалитися во хвале Твоей.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Благословен Господь Бог Израилев от века и до века. И рекут вси людие: буди, буди.

< Zabura 106 >