< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
alleluia confitemini Domino quoniam bonus quoniam in saeculum misericordia eius
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
quis loquetur potentias Domini auditas faciet omnes laudes eius
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
beati qui custodiunt iudicium et faciunt iustitiam in omni tempore
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
memento nostri Domine in beneplacito populi tui visita nos in salutari tuo
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
ad videndum in bonitate electorum tuorum ad laetandum in laetitia gentis tuae et lauderis cum hereditate tua
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
peccavimus cum patribus nostris iniuste egimus iniquitatem fecimus
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
patres nostri in Aegypto non intellexerunt mirabilia tua non fuerunt memores multitudinis misericordiae tuae et inritaverunt ascendentes in mare mare; Rubrum
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
et salvavit eos propter nomen suum ut notam faceret potentiam suam
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
et increpuit mare Rubrum et exsiccatum est et deduxit eos in abyssis sicut in deserto
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
et salvavit eos de manu odientium et redemit eos de manu inimici
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
et operuit aqua tribulantes eos unus ex eis non remansit
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
et crediderunt in verbis eius et laudaverunt laudem eius
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
cito fecerunt obliti sunt operum eius non sustinuerunt consilium eius
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
et concupierunt concupiscentiam in deserto et temptaverunt Deum in inaquoso
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
et dedit eis petitionem ipsorum et misit saturitatem in anima eorum
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
et inritaverunt Mosen in castris Aaron sanctum Domini
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
aperta est terra et degluttivit Dathan et operuit super congregationem Abiron
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
et exarsit ignis in synagoga eorum flamma conbusit peccatores
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
et fecerunt vitulum in Choreb et adoraverunt sculptile
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
et mutaverunt gloriam suam in similitudine vituli comedentis faenum
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
obliti sunt Deum qui salvavit eos qui fecit magnalia in Aegypto
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
mirabilia in terra Cham terribilia in mari Rubro
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
et dixit ut disperderet eos si non Moses electus eius stetisset in confractione in conspectu eius ut averteret iram eius ne disperderet eos
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
et pro nihilo habuerunt terram desiderabilem non crediderunt verbo eius
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
et murmurabant in tabernaculis suis non exaudierunt vocem Domini
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
et elevavit manum suam super eos ut prosterneret eos in deserto
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
et ut deiceret semen eorum in nationibus et dispergeret eos in regionibus
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
et initiati sunt Beelphegor et comederunt sacrificia mortuorum
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
et inritaverunt eum in adinventionibus suis et multiplicata est in eis ruina
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
et stetit Finees et placavit et cessavit quassatio
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
et reputatum est ei in iustitiam in generatione et generationem usque in sempiternum
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
et inritaverunt ad aquam Contradictionis et vexatus est Moses propter eos
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
quia exacerbaverunt spiritum eius et distinxit in labiis suis
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
non disperdiderunt gentes quas dixit Dominus illis
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
et commixti sunt inter gentes et didicerunt opera eorum
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
et servierunt sculptilibus eorum et factum est illis in scandalum
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
et immolaverunt filios suos et filias suas daemoniis
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
et effuderunt sanguinem innocentem sanguinem filiorum suorum et filiarum suarum; quas sacrificaverunt sculptilibus Chanaan et interfecta est terra in sanguinibus
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
et contaminata est in operibus eorum et fornicati sunt in adinventionibus suis
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
et iratus est furore Dominus in populo suo et abominatus est hereditatem suam
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
et tradidit eos in manus gentium et dominati sunt eorum qui oderant eos
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
et tribulaverunt eos inimici eorum et humiliati sunt sub manibus eorum
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
saepe liberavit eos ipsi autem exacerbaverunt eum in consilio suo et humiliati sunt in iniquitatibus suis
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
et vidit cum tribularentur et audiret orationem eorum
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
et memor fuit testamenti sui et paenituit eum secundum multitudinem misericordiae suae
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
et dedit eos in misericordias in conspectu omnium qui ceperant eos
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
salvos fac nos Domine Deus noster et congrega nos de nationibus ut confiteamur nomini tuo sancto et gloriemur in laude tua
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
benedictus Dominus Deus Israhel a saeculo et usque in saeculum et dicet omnis populus fiat fiat