< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alleluia. Confitemini Domino quoniam bonus: quoniam in sæculum misericordia eius.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Quis loquetur potentias Domini, auditas faciet omnes laudes eius?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Beati, qui custodiunt iudicium, et faciunt iustitiam in omni tempore.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Memento nostri Domine in beneplacito populi tui: visita nos in salutari tuo:
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Ad videndum in bonitate electorum tuorum, ad lætandum in lætitia gentis tuæ: ut lauderis cum hereditate tua.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Peccavimus cum patribus nostris: iniuste egimus, iniquitatem fecimus.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Patres nostri in Ægypto non intellexerunt mirabilia tua: non fuerunt memores multitudinis misericordiæ tuæ. Et irritaverunt ascendentes in mare, Mare Rubrum.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Et salvavit eos propter nomen suum: ut notam faceret potentiam suam.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Et increpuit Mare Rubrum, et exiccatum est: et deduxit eos in abyssis sicut in deserto.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Et salvavit eos de manu odientium: et redemit eos de manu inimici.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Et operuit aqua tribulantes eos: unus ex eis non remansit.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Et crediderunt verbis eius: et laudaverunt laudem eius.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Cito fecerunt, obliti sunt operum eius: et non sustinuerunt consilium eius.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Et concupierunt concupiscentiam in deserto: et tentaverunt Deum in inaquoso.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Et dedit eis petitionem ipsorum: et misit saturitatem in animas eorum.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Et irritaverunt Moysen in castris: Aaron sanctum Domini.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Aperta est terra, et deglutivit Dathan: et operuit super congregationem Abiron.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Et exarsit ignis in synagoga eorum: flamma combussit peccatores.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Et fecerunt vitulum in Horeb: et adoraverunt sculptile.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Et mutaverunt gloriam suam in similitudinem vituli comedentis fœnum.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Obliti sunt Deum, qui salvavit eos, qui fecit magnalia in Ægypto,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
mirabilia in Terra Cham: terribilia in Mari Rubro.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Et dixit ut disperderet eos: si non Moyses electus eius stetisset in confractione in conspectu eius: Ut averteret iram eius ne disperderet eos:
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
et pro nihilo habuerunt terram desiderabilem: Non crediderunt verbo eius,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
et murmuraverunt in tabernaculis suis: non exaudierunt vocem Domini.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Et elevavit manum suam super eos: ut prosterneret eos in deserto:
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Et ut deiiceret semen eorum in Nationibus: et dispergeret eos in regionibus.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Et initiati sunt Beelphegor: et comederunt sacrificia mortuorum.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Et irritaverunt eum in adinventionibus suis: et multiplicata est in eis ruina.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Et stetit Phinees, et placavit: et cessavit quassatio.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Et reputatum est ei in iustitiam, in generationem et generationem usque in sempiternum.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Et irritaverunt eum ad Aquas Contradictionis: et vexatus est Moyses propter eos:
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
quia exacerbaverunt spiritum eius. Et distinxit in labiis suis:
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
non disperdiderunt gentes, quas dixit Dominus illis.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Et commisti sunt inter Gentes, et didicerunt opera eorum:
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
et servierunt sculptilibus eorum: et factum est illis in scandalum.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Et immolaverunt filios suos, et filias suas dæmoniis.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Et effuderunt sanguinem innocentem: sanguinem filiorum suorum et filiarum suarum, quas sacrificaverunt sculptilibus Chanaan. Et infecta est terra in sanguinibus,
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
et contaminata est in operibus eorum: et fornicati sunt in adinventionibus suis.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Et iratus est furore Dominus in populum suum: et abominatus est hereditatem suam.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Et tradidit eos in manus gentium: et dominati sunt eorum qui oderunt eos.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Et tribulaverunt eos inimici eorum, et humiliati sunt sub manibus eorum:
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
sæpe liberavit eos. Ipsi autem exacerbaverunt eum in consilio suo: et humiliati sunt in iniquitatibus suis.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Et vidit cum tribularentur: et audivit orationem eorum.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Et memor fuit testamenti sui: et pœnituit eum secundum multitudinem misericordiæ suæ.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Et dedit eos in misericordias in conspectu omnium qui ceperant eos.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Salvos nos fac Domine Deus noster: et congrega nos de Nationibus: Ut confiteamur nomini sancto tuo: et gloriemur in laude tua.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Benedictus Dominus Deus Israel a sæculo et usque in sæculum: et dicet omnis populus: Fiat, fiat.

< Zabura 106 >