< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Hallelujah! Danket dem HERRN, denn er ist gütig, seine Gnade währt ewiglich!
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Wer kann die Machttaten des HERRN beschreiben und allen seinen Ruhm verkünden?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Wohl denen, die das Recht beachten, die Gerechtigkeit üben allezeit!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Gedenke meiner, o HERR, aus Gnaden gegen dein Volk, suche mich heim mit deinem Heil,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
daß ich einen Einblick bekomme in das Wohlergehen deiner Auserwählten, mich freue an der Freude deines Volkes und mich deines Erbteils rühme.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Wir haben gesündigt samt unsern Vätern, wir haben verkehrt gehandelt, wir haben gefrevelt.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Unsre Väter in Ägypten hatten nicht acht auf deine Wunder, sie gedachten nicht an die Größe deiner Güte und waren widerspenstig am Meer, am Schilfmeer.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Aber er half ihnen um seines Namens willen, um seine Stärke kundzutun.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Und er bedrohte das Schilfmeer, daß es vertrocknete, und ließ sie durch die Tiefen gehen wie auf einer Steppe.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Und er rettete sie von der Hand des Hassers und erlöste sie aus der Hand des Feindes.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Und das Wasser bedeckte ihre Bedränger, nicht einer von ihnen blieb übrig.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Da glaubten sie seinen Worten und sangen sein Lob.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Aber sie vergaßen seine Werke bald, sie warteten nicht auf seinen Rat,
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
sondern ließen sich gelüsten in der Wüste und versuchten Gott in der Einöde.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Und er gab ihnen, was sie forderten, sandte aber eine Seuche unter sie.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Und sie wurden eifersüchtig auf Mose im Lager, auf Aaron, den Heiligen des HERRN.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Da tat sich die Erde auf und verschlang Datan und bedeckte die Rotte Abirams;
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
und Feuer verzehrte ihre Rotte, die Flamme versengte die Gottlosen.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Sie machten ein Kalb am Horeb und warfen sich nieder vor dem gegossenen Bild.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Sie vertauschten ihre Herrlichkeit gegen das Abbild eines Stiers, der Gras frißt.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Sie vergaßen Gottes, ihres Retters, der große Dinge in Ägypten getan,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wunder im Lande Hams, Furchtbares am Schilfmeer.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Und er gedachte sie zu vertilgen, wenn nicht Mose, sein Auserwählter, in den Riß getreten wäre vor seinem Angesicht, um seinen Grimm abzuwenden, daß er sie nicht vertilgte.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Sie verachteten das liebliche Land, sie glaubten seinem Worte nicht.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Und sie murrten in ihren Zelten, sie gehorchten nicht der Stimme des HERRN.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Da erhob er seine Hand [und schwur], sie niederzustrecken in der Wüste
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
und ihren Samen unter die Nationen zu werfen und sie zu zerstreuen in die Länder.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Und sie hängten sich an den Baal-Peor und aßen Opfer der toten [Götzen],
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
und sie erzürnten ihn mit ihrem Tun; da brach die Plage unter ihnen aus.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Aber Pinehas trat auf und übte Gericht, so daß die Plage aufgehalten ward.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Das wurde ihm zur Gerechtigkeit gerechnet auf alle Geschlechter, in Ewigkeit.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Und sie erzürnten ihn am Haderwasser, und es erging Mose übel um ihretwillen.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Denn sie betrübten seinen Geist, und er redete unbedacht mit seinen Lippen.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Sie vertilgten die Völker nicht, von denen der HERR ihnen gesagt hatte;
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
sondern ließen sich ein mit den Heiden und lernten ihre Weise.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Und sie dienten ihren Götzen, und diese wurden ihnen zum Fallstrick.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Und sie opferten ihre Söhne und ihre Töchter den bösen Geistern.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Und sie vergossen unschuldiges Blut, das Blut ihrer Söhne und ihrer Töchter, welche sie den Götzen Kanaans opferten, und so wurde das Land durch Blutschulden entweiht.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Und sie befleckten sich mit ihren Werken und hurten mit ihrem Tun.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Da entbrannte der Zorn des HERRN wider sein Volk, und er faßte einen Abscheu gegen sein Erbe.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Und er gab sie in die Hand der Nationen, daß ihre Hasser über sie herrschten.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Und ihre Feinde bedrückten sie, und sie wurden gedemütigt unter ihre Hand.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Er errettete sie oftmals; aber sie widerstrebten ihm mit ihren Anschlägen und kamen herunter durch eigene Schuld.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Aber er sah ihre Not an, als er ihr Schreien hörte,
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
und gedachte seines Bundes mit ihnen und empfand Mitleid nach seiner großen Huld
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
und ließ sie Erbarmen finden bei denen, die sie gefangen hielten.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Hilf uns, HERR, unser Gott, sammle uns aus den Heiden, daß wir deinem heiligen Namen danken und uns glücklich preisen, zu deinem Ruhm!
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Gelobt sei der HERR, der Gott Israels, von Ewigkeit zu Ewigkeit, und alles Volk soll sagen: Amen! Hallelujah!

< Zabura 106 >