< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Halleluja! Preiset den HERRN, denn er ist freundlich, ja ewiglich währt seine Gnade!
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Wer kann des HERRN Machttaten gebührend preisen und kundtun all seinen Ruhm?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Wohl denen, die am Recht festhalten, und dem, der Gerechtigkeit übt zu jeder Zeit!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Gedenke meiner, o HERR, mit der Liebe zu deinem Volk, nimm dich meiner an mit deiner Hilfe,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
daß ich schau’ meine Lust am Glück deiner Erwählten, an der Freude deines Volkes Anteil habe und glücklich mich preise mit deinem Eigentumsvolke!
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Wir haben gesündigt gleich unsern Vätern, wir haben gefehlt und gottlos gehandelt.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Unsre Väter in Ägypten achteten nicht auf deine Wunder, gedachten nicht der Fülle deiner Gnadenerweise, waren widerspenstig gegen den Höchsten schon am Schilfmeer;
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
dennoch half er ihnen um seines Namens willen, um seine Heldenkraft zu erweisen.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Er schalt das Schilfmeer: da ward es trocken, und er ließ sie ziehn durch die Fluten wie über die Trift.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
So rettete er sie aus der Hand des Verfolgers und erlöste sie aus der Gewalt des Feindes:
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
die Fluten bedeckten ihre Bedränger, nicht einer von ihnen blieb übrig.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Da glaubten sie an seine Worte, besangen seinen Ruhm.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Doch schnell vergaßen sie seine Taten und warteten seinen Ratschluß nicht ab;
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
sie fröhnten ihrem Gelüst in der Wüste und versuchten Gott in der Einöde:
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
da gewährte er ihnen ihr Verlangen, sandte aber die Seuche gegen ihr Leben.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Dann wurden sie eifersüchtig auf Mose im Lager, auf Aaron, den Geweihten des HERRN:
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
da tat die Erde sich auf und verschlang Dathan und begrub die ganze Rotte Abirams,
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Feuer verbrannte ihre Rotte, Flammen verzehrten die Frevler.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Sie machten sich ein Kalb am Horeb und warfen vor einem Gußbild sich nieder
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
und vertauschten so die Herrlichkeit ihres Gottes mit dem Bildnis eines Stieres, der Gras frißt.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Sie hatten Gott, ihren Retter, vergessen, der große Dinge getan in Ägypten,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wunderzeichen im Lande Hams, furchtbare Taten am Schilfmeer.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Da gedachte er sie zu vertilgen, wenn nicht Mose, sein Auserwählter, mit Fürbitte vor ihn hingetreten wäre, um seinen Grimm vom Vernichten abzuwenden.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Sodann verschmähten sie das herrliche Land und schenkten seiner Verheißung keinen Glauben,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
sondern murrten in ihren Zelten, gehorchten nicht der Weisung des HERRN.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Da erhob er seine Hand gegen sie zum Schwur, sie in der Wüste niederzuschlagen,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
ihre Nachkommen unter die Heiden niederzuwerfen und sie rings zu zerstreuen in die Länder.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Dann hängten sie sich an den Baal-Peor und aßen Opferfleisch der toten (Götzen)
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
und erbitterten ihn durch ihr ganzes Tun. Als nun ein Sterben unter ihnen ausbrach,
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
trat Pinehas auf und hielt Gericht: da wurde dem Sterben Einhalt getan.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Das wurde ihm angerechnet zur Gerechtigkeit von Geschlecht zu Geschlecht in Ewigkeit. –
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Dann erregten sie Gottes Zorn am Haderwasser, und Mose erging es übel um ihretwillen;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
denn weil sie dem Geiste Gottes widerstrebten, hatte er unbedacht mit seinen Lippen geredet.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Sie vertilgten auch die Völker nicht, von denen der HERR es ihnen geboten,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
sondern traten mit den Heiden in Verkehr und gewöhnten sich an deren (böses) Tun
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
und dienten ihren Götzen: die wurden ihnen zum Fallstrick.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Ja, sie opferten ihre Söhne und ihre Töchter den bösen Geistern
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
und vergossen unschuldig Blut [das Blut ihrer Söhne und Töchter, die sie den Götzen Kanaans opferten]: so wurde das Land durch Blutvergießen entweiht.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Sie wurden unrein durch ihr Verhalten und verübten Abfall durch ihr Tun. –
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Da entbrannte der Zorn des HERRN gegen sein Volk, und Abscheu fühlte er gegen sein Erbe;
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
er ließ sie in die Hand der Heiden fallen, so daß ihre Hasser über sie herrschten;
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
ihre Feinde bedrängten sie hart, so daß sie sich beugen mußten unter deren Hand.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Oftmals zwar befreite er sie, doch sie blieben widerspenstig gegen seinen Ratschluß und sanken immer tiefer durch ihre Schuld.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Er aber nahm sich ihrer Drangsal an, sooft er ihr Wehgeschrei hörte,
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
und gedachte seines Bundes ihnen zugut, fühlte Mitleid nach seiner großen Güte
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
und ließ sie Erbarmen finden bei allen, die sie gefangen hielten.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
O hilf uns, HERR, unser Gott, und bring uns wieder zusammen aus den Heiden, damit wir deinem heiligen Namen danken, uns glücklich preisen, deinen Ruhm zu künden!
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Gepriesen sei der HERR, der Gott Israels, von Ewigkeit zu Ewigkeit! Und alles Volk sage »Amen!« Halleluja!