< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Rühmet Jah! Danket Jahwe, denn er ist gütig; denn ewig währt seine Gnade.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Wer kann die Machtthaten Jahwes ausreden, all seinen Ruhm verkündigen?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Wohl denen, die auf Recht halten, dem, der zu jeder Zeit Gerechtigkeit übt.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Gedenke meiner, Jahwe, nach der Huld, die du deinem Volke verheißen; suche mich heim mit deiner Hilfe,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
daß ich am Glücke deiner Auserwählten meine Lust schaue, mich an der Freude deines Volkes freue, mit deinem Eigentum mich rühme!
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Wir haben gesündigt samt unsern Vätern, haben uns verschuldet, sind gottlos gewesen.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Unsere Väter in Ägypten begriffen deine Wunder nicht, gedachten nicht an deine große Gnade und empörten sich wider den Höchsten am Schilfmeer.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Aber er half ihnen um seines Namens willen, um seine Stärke kund zu thun.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Er bedrohte das Schilfmeer, daß es vertrocknete, und führte sie durch die Fluten wie auf einer Trift.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Er rettete sie aus der Gewalt dessen, der sie haßte, und befreite sie aus der Gewalt des Feindes.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Die Gewässer bedeckten ihre Bedränger; kein einziger von ihnen blieb übrig.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Da glaubten sie an seine Worte, sangen seinen Ruhm.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Eilends vergaßen sie seine Thaten, warteten nicht auf seinen Entschluß.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Sie verfielen in der Steppe auf ein Gelüst und versuchten Gott in der Einöde.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Da gab er ihnen, was sie begehrten, und ließ die Darre in sie kommen.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Und sie wurden eifersüchtig auf Mose im Lager, auf Aaron, den Heiligen Jahwes.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Die Erde that sich auf und verschlang Dathan und bedeckte die Rotte Abirams.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Und Feuer zündete unter ihrer Rotte, die Flamme verbrannte die Gottlosen.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Sie machten ein Kalb am Horeb und warfen sich nieder vor einem Gußbild
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
und vertauschten ihren Herrlichen mit dem Bild eines Stiers, der Gras frißt.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Sie vergaßen Gottes, ihres Erretters, der Großes in Ägypten gethan hatte,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wunderbares im Lande Hams, Furchtbares am Schilfmeer.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Da gedachte er, sie zu vertilgen, wenn nicht Mose, sein Auserwählter, vor ihm in die Bresche getreten wäre, um seinen Grimm vom Vertilgen wieder abzubringen.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Sie verschmähten das wonnige Land und glaubten seinem Worte nicht.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Sie murrten in ihren Zelten, hörten nicht auf die Stimme Jahwes.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Da erhob er ihnen seine Hand und schwur, daß er sie in der Wüste fällen
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
und ihre Nachkommen unter die Völker zerstreuen und in die Länder versprengen wolle.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Sie hingen sich an Baal Peor und aßen von den Opfern der toten Götzen.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Und sie erzürnten ihn durch ihre Thaten; da fuhr eine Plage unter sie.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Pinehas aber trat auf und richtete, da ward der Plage Einhalt gethan.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Und das wurde ihm als Gerechtigkeit zugerechnet durch alle folgenden Geschlechter bis in Ewigkeit.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Sodann erzürnten sie Gott am Hader-Wasser, und es erging Mose um ihretwillen übel.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Denn sie hatten seinem Geiste widerstrebt, und er redete unbedacht mit seinen Lippen.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Sie vertilgten nicht die Völker, die zu vertilgen Jahwe ihnen befohlen hatte.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Sie ließen sich mit den Heiden ein und lernten ihre Werke;
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
sie dienten ihren Götzen, und sie wurden ihnen zum Fallstrick.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Sie opferten Söhne und Töchter den Dämonen
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
und vergossen unschuldiges Blut, das Blut ihrer Söhne und Töchter, die sie den Götzen Kanaans opferten, daß das Land durch Blutschuld entweiht ward.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Sie verunreinigten sich durch ihre Werke und verübten Buhlerei mit ihren Thaten.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Da entbrannte der Zorn Jahwes gegen sein Volk, und er verabscheute sein Eigentum.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Er überlieferte sie in die Gewalt der Heiden, daß ihre Hasser über sie herrschten.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Und ihre Feinde bedrückten sie, und sie wurden unter ihre Gewalt gebeugt.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Viele Male errettete er sie; sie aber waren widerspenstig in ihrem Vorhaben und sanken durch ihre Verschuldung.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Und er sah ihre Not an, als er ihr Flehen vernahm,
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
und gedachte ihnen zu gut an seinen Bund und ließ sich's leid sein nach seiner großen Gnade.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Er schaffte, daß sie Erbarmen fanden bei allen, die sie gefangen hielten.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Hilf uns, Jahwe, unser Gott, und sammle uns aus den Heiden, daß wir deinem heiligen Namen danken, uns deines Lobpreises rühmen!
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Gepriesen sei Jahwe, der Gott Israels, von Ewigkeit bis zu Ewigkeit, und alles Volk spreche: Amen! Rühmet Jah!