< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Lobet Jah! / Danket Jahwe, denn er ist gütig; / Ewig währet ja seine Huld.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Wer kann gebührend von Jahwes Taten reden / Und all seinen Ruhm erschöpfend verkünden?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Heil denen, die das Gesetz befolgen, / Die Gerechtigkeit üben zu jeder Zeit!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Gedenke mein, o Jahwe! / Auch mir schenk die Huld, die dein Volk erfährt! / Auch mich sieh an, wenn du ihm hilfst!
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Dann schau ich mit Lust deiner Erwählten Glück, / Dann teil ich die Freude deines Volks / Und darf mich rühmen mit deinem Erbe.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Wir haben gesündigt gleich unsern Vätern, / Haben gottlos gehandelt, gefrevelt.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Unsre Väter in Ägypten achteten nicht deiner Wunder, / Gedachten nicht deiner Gnadenfülle, / Sondern waren widerspenstig am Meer, am Schilfmeer.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Er aber rettete sie um seines Namens willen, / Um seine Macht zu beweisen.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Er schalt das Schilfmeer, da ward es trocken. / In den Fluten ließ er sie ziehn wie auf blachem Feld.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
So befreite er sie aus des Hassers Hand / Und erlöste sie aus des Feindes Gewalt.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Die Wasser bedeckten ihre Bedränger: / Nicht einer von ihnen blieb übrig.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Da vertrauten sie auf seine Worte, / Sie sangen seinen Ruhm.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Doch schnell vergaßen sie seine Taten, / Warteten nicht, daß sein Rat sich erfülle.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Sondern lüstern wurden sie in der Wüste / Und versuchten Gott in der Öde.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Da erfüllte er wohl ihr Verlangen, / Aber dann sandte er ihnen Krankheit zu.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Sie waren auch neidisch auf Mose im Lager, / Auf Aaron, Jahwes Geweihten.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Da tat sich die Erde auf: sie verschlang Datan / Und bedeckte die Rotte Abirams.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Feuer ergriff ihre Rotte, / Die Flamme verzehrte die Frevler.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Sie machten ein Kalb am Horeb / Und beteten dann dies Gußbild an.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Ihres Gottes Herrlichkeit gaben sie hin / Für das Bild eines Stieres, der Gras frißt.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Sie hatten Gott, ihren Retter, vergessen, / Der Großes getan in Ägypten,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wunder im Lande Hams, / Erstaunliche Dinge am Schilfmeer.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Er wollte sie schon vertilgen: / Doch da trat Mose, sein Auserwählter, vor ihm in den Riß, / Um seine Zornglut abzuwenden, / Daß er sie nicht verderbe.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Sie verschmähten das köstliche Land, / Sie trauten seiner Verheißung nicht,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Sondern murrten in ihren Zelten, / Gehorchten nicht Jahwes Stimme.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Da hub er auf seine Hand und schwur, / Sie niederzuschlagen in der Wüste,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Ihre Nachkommen unter die Völker zu werfen, / Sie zu zerstreuen in die Länder.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Sie hängten sich an den Baal Peôr / Und aßen Opfer für Tote.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
So reizten sie ihn mit ihrem Tun. / Da riß unter ihnen ein Sterben ein.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Nun aber trat Pinehas auf und hielt Gericht: / Da ward der Plage Einhalt getan.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Das ward ihm gerechnet zur Gerechtigkeit / Für alle Geschlechter, für immer.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Sie erzürnten ihn weiter am Haderwasser, / Und übel ging's Mose um ihretwillen.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Denn sie hatten seinem Geist widerstrebt, / So daß ihm unbedachte Worte entfuhren.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Sie vertilgten auch nicht die Völker, / Wie ihnen Jahwe geboten hatte.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Sondern sie ließen sich ein mit den Heiden / Und nahmen an ihrem Treiben teil:
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Sie dienten ihren Götzen, / Die wurden ihnen zum Fallstrick.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Sie opferten ihre Söhne / Und ihre Töchter den bösen Geistern.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
So vergossen sie schuldlos Blut, / Das Blut ihrer Söhne und Töchter, / Die sie opferten Kanaans Götzen, / Daß das Land durch Blutschuld entweiht ward.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
So wurden sie unrein durch ihr Tun / Und fielen von Gott durch ihr Treiben ab.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Da entbrannte Jahwes Zorn wider sein Volk, / Er fühlte Abscheu gegen sein Erbe.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Drum gab er sie in der Heiden Hand, / Daß ihre Hasser über sie herrschten.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Ihre Feinde bedrängten sie, / Sie mußten sich beugen ihrer Gewalt.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Oftmals zwar befreite er sie, / Doch in Eigensinn lehnten sie sich auf: / Drum gingen sie unter in ihrer Schuld.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Er aber sah gnädig auf ihre Not, / Als er ihr lautes Schrein vernahm.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Da gedachte er ihnen an seinen Bund / Und hatte Mitleid in großer Huld.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Er ließ sie Erbarmen finden / Bei allen, die sie ins Elend geführt.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Hilf uns, Jahwe, unser Gott, / Und sammle uns aus den Heiden! / Dann wollen wir danken deinem heiligen Namen, / Uns glücklich preisen, dich zu loben.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Gepriesen sei Jahwe, Israels Gott, / Von Ewigkeit zu Ewigkeit! / Und alles Volk spreche: / "Ja wahrlich! Lobt Jah!"