< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Louez l'Eternel. Célébrez l'Eternel; car il [est] bon, parce que sa bonté demeure à toujours.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Qui pourrait réciter les exploits de l'Eternel? Qui pourrait faire retentir toute sa louange?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Ô que bienheureux sont ceux qui observent la justice, [et] qui font en tout temps ce qui est juste!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Eternel, souviens-toi de moi selon la bienveillance que tu portes à ton peuple, et aie soin de moi selon ta délivrance.
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Afin que je voie le bien de tes élus, que je me réjouisse dans la joie de ta nation, [et] que je me glorifie avec ton héritage.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Nous avons péché avec nos pères, nous avons agi iniquement, nous avons mal fait.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nos pères n'ont point été attentifs à tes merveilles en Egypte; ils ne se sont point souvenus de la multitude de tes faveurs; mais ils ont été rebelles auprès de la mer, vers la mer Rouge.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Toutefois il les délivra pour l'amour de son Nom, afin de donner à connaître sa puissance.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Car il tança la mer Rouge, et elle se sécha, et il les conduisit par les gouffres comme par le désert;
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Et les délivra de la main de ceux qui [les] haïssaient, et les garantit de la main de l'ennemi.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Et les eaux couvrirent leurs oppresseurs, il n'en resta pas un seul.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Alors ils crurent à ses paroles, [et] ils chantèrent sa louange.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
[Mais] ils mirent incontinent en oubli ses œuvres, et ne s'attendirent point à son conseil.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Mais ils furent épris de convoitise au désert, et ils tentèrent le [Dieu] Fort au lieu inhabitable.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Alors il leur donna ce qu'ils avaient demandé, toutefois il leur envoya une phtisie en leur corps.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Ils portèrent envie à Moïse dans le camp, [et] à Aaron le saint de l'Eternel.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
La terre s'ouvrit, et engloutit Dathan, et couvrit la bande d'Abiram.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Aussi le feu s'alluma en leur assemblée, [et] la flamme brûla les méchants.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Ils firent un veau en Horeb, et se prosternèrent devant l'image de fonte.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Ils changèrent leur gloire en la figure d'un bœuf qui mange l'herbe.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Ils oublièrent le [Dieu] Fort, leur Libérateur, qui avait fait de grandes choses en Egypte;
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Des choses merveilleuses au pays de Cam, et des choses terribles sur la mer Rouge.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
C'est pourquoi il dit qu'il les détruirait; mais Moïse son élu se tint à la brèche devant lui, pour détourner sa fureur, afin qu'il ne [les] défît point.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Ils méprisèrent le pays désirable, [et] ne crurent point à sa parole.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Et ils se mutinèrent dans leurs tentes, et n'obéirent point à la voix de l'Eternel.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
C'est pourquoi il leur jura la main levée, qu'il les renverserait dans le désert,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Et qu'il accablerait leur postérité parmi les nations, et qu'il les disperserait par les pays.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Ils se joignirent aux adorateurs de Bahal-Péhor, et mangèrent des sacrifices des morts.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Et ils dépitèrent [Dieu] par les choses à quoi ils s'adonnèrent, tellement qu'une plaie fit brèche sur eux.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Mais Phinées se présenta, et fit justice; et la plaie fut arrêtée.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Et cela lui a été alloué pour justice dans tous les âges à jamais.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Ils excitèrent aussi sa colère près des eaux de Mériba, et il en avint du mal à Moïse à cause d'eux.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Car ils chagrinèrent son esprit, et il parla légèrement de ses lèvres.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Ils n'ont point détruit les peuples que l'Eternel leur avait dit;
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Mais ils se sont mêlés parmi ces nations, et ils ont appris leurs manières de faire;
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Et ont servi à leurs faux dieux, lesquels leur ont été en pièges.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Car ils ont sacrifié leurs fils et leurs filles aux démons.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Et ils ont répandu le sang innocent, le sang de leurs fils et de leurs filles, lesquels ils ont sacrifiés aux faux dieux de Canaan; et le pays a été souillé de sang.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Et ils ont été souillés par leurs œuvres, et ont paillardé par les choses à quoi ils se sont adonnés.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
C'est pourquoi la colère de l'Eternel s'est embrasée contre son peuple, et il a eu en abomination son héritage.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Et il les a livrés entre les mains des nations, et ceux qui les haïssaient, ont dominé sur eux.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Et leurs ennemis les ont opprimés, et ils ont été humiliés sous leur main.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Il les a souvent délivrés, mais ils l'ont irrité par leur conseil, et ils ont été mis en langueur par leur iniquité.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Toutefois il les a regardés dans leur détresse, quand il entendait leur clameur.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Et il s'est souvenu en leur faveur de son alliance, et s'est repenti selon la grandeur de ses compassions.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Et il a fait que ceux qui les avaient emmenés captifs, ont eu pitié d'eux.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Eternel notre Dieu, délivre-nous et nous recueille d'entre les nations, afin que nous célébrions le Nom de ta sainteté, et que nous nous glorifiions en ta louange.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Béni soit l'Eternel, le Dieu d'Israël, depuis un siècle jusqu’à l'autre siècle! et que tout le peuple dise, Amen! Louez l'Eternel.

< Zabura 106 >