< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alléluiah! Rendez grâces au Seigneur, parce qu'il est bon, parce que sa miséricorde est éternelle.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Qui dira la puissance du Seigneur, qui fera entendre toutes ses louanges?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Heureux ceux qui gardent ses jugements et qui font justice en tout temps!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Souviens-toi de nous, Seigneur, avec ta bonté pour ton peuple; visite- nous avec ton salut;
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Afin que nous puissions avoir part aux biens de tes élus, nous réjouir de la joie de ton peuple, te glorifier avec ceux de ton héritage.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Nous avons péché avec nos pères, nous avons violé ta loi, nous avons commis l'iniquité.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nos pères en Egypte ne comprirent point tes prodiges, et ils ne se souvinrent pas de l'abondance de ta miséricorde; et ils te provoquèrent, en arrivant à la mer Rouge.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Et il les sauva pour la gloire de son nom, et pour manifester sa puissance.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Et il menaça la mer Rouge, et elle fut desséchée; et il les ramena dans l'abîme, comme dans le désert.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Et il les sauva des mains de ceux qui les haïssaient, et il les racheta de la main de l'ennemi.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
L'eau couvrit ceux qui les opprimaient, et pas un d'eux n'échappa.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Et ils eurent foi en ses paroles, et ils chantèrent ses louanges.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Mais ils oublièrent bien vite ses œuvres; ils n'attendirent point son conseil.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Et ils furent pris de concupiscence dans la solitude, et ils tentèrent Dieu dans le désert sans eau.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Et il leur accorda ce qu'ils demandaient, et il envoya la satiété dans leur âme.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Et ils irritèrent Moïse dans le camp, et Aaron le saint du Seigneur.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
La terre s'ouvrit, et elle engloutit Dathan, et engouffra le rassemblement d'Abiron.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Et la flamme dévora leur synagogue, et le feu consuma les pécheurs.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Et ils se firent un veau en Choreb, et ils adorèrent une image sculptée.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Et ils échangèrent leur gloire contre la statue d'un veau qui se repaît de fourrage.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Ils oublièrent le Dieu qui les avait sauvés, qui avait fait de grandes choses en Egypte,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Des prodiges en la terre de Cham, et des actions terribles sur la mer Rouge.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Et il dit qu'il les exterminerait, si Moïse, son élu, ne s'était placé devant lui, et n'eût brisé l'idole, pour détourner sa fureur et l'empêcher de les détruire.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Et ils méprisèrent comme rien la terre désirable, et n'eurent point foi en la parole de Dieu.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Et ils murmurèrent sous leurs tentes, et n'écoutèrent point la voix du Seigneur!
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Et il leva la main sur eux pour les abattre dans le désert,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
Et pour rejeter leur race parmi les nations, et les disperser en diverses régions.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Et ils se prostituèrent à Belphégor, et ils mangèrent des victimes sacrifiées aux morts.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Et ils irritèrent Dieu par leurs désordres, et la ruine se multiplia chez eux.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Et Phinéès se leva, et il apaisa le Seigneur, et la plaie cessa.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Et cela lui fut imputé à justice, de génération en génération, dans tous les siècles.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Et ils irritèrent Dieu vers les eaux de contradiction, et Moïse eut à souffrir de leur part;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Parce qu'ils avaient rempli son esprit d'une amertume qui s'échappa de ses lèvres.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Ils n'exterminèrent point les nations, comme le Seigneur le leur avait dit;
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Et ils se mêlèrent aux Gentils, et ils apprirent leurs œuvres,
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
Et ils servirent leurs idoles, et ce fut pour eux un sujet de chute.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Et ils sacrifièrent aux démons leurs fils et leurs filles.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
Et ils versèrent le sang innocent, le sang de leurs fils et de leurs filles, qu'ils immolèrent aux sculptures de Chanaan. Et la terre fut pleine de carnage et de sang.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Et elle fut souillée par leurs œuvres; et ils se prostituèrent en leurs passions.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Et le Seigneur s'enflamma de colère contre son peuple, et il eut en abomination son héritage.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Et il les livra aux mains de leurs ennemis, et ceux qui les haïssaient devinrent leurs maîtres.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Et leurs ennemis les opprimèrent, et ils furent humiliés sous leurs mains.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Souvent Dieu les sauva; mais ils l'irritèrent encore en leurs conseils, et ils furent humiliés dans leurs iniquités.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Et le Seigneur les vit en leurs tribulations, et il écouta leur prière.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Et il se souvint de son alliance, et il se repentit en la plénitude de sa miséricorde.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Et il leur accorda ses miséricordes, en face de ceux qui les retenaient captifs.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Sauve-nous, Seigneur notre Dieu, et rassemble-nous du milieu des Gentils, pour que nous proclamions ton saint nom et que nous mettions notre gloire à te louer.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Béni soit le Seigneur, Dieu d'Israël, dans tous les siècles des siècles, et tout le peuple dira: Ainsi soit-il! Ainsi soit-il!

< Zabura 106 >