< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alléluia! Rendez hommage à l’Eternel, car sa grâce dure à jamais.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Qui saura dire la toute-puissance de l’Eternel, exprimer toute sa gloire?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Heureux ceux qui respectent le droit, pratiquent la justice en tout temps!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Souviens-toi de moi, ô Eternel, dans ta bienveillance pour ton peuple, veille sur moi, par ta protection,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
pour que je puisse voir le bonheur de tes élus, me réjouir de la joie de ton peuple, me glorifier de concert avec ton héritage.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Nous avons péché tout comme nos pères, nous avons mal agi, nous sommes coupables!
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Nos pères, en Egypte, n’ont pas compris tes miracles, ni gardé le souvenir de tes nombreux bienfaits! Ils se révoltèrent aux bords de la mer, de la mer des Joncs.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Lui cependant les secourut à cause de son nom, pour faire connaître sa puissance.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Il apostropha la mer des Joncs, et elle se dessécha, il leur fit traverser les flots comme une terre nue.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
Il leur porta secours contre l’oppresseur, les délivra de la main de l’ennemi.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Les eaux recouvrirent leurs persécuteurs, pas un d’entre eux n’en réchappa.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Alors ils eurent foi en ses paroles, et chantèrent ses louanges.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Bien vite ils oublièrent ses œuvres; ils ne mirent pas leur attente dans ses desseins.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Ils furent pris d’ardentes convoitises dans le désert, et mirent Dieu à l’épreuve dans la solitude.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
Il leur accorda ce qu’ils réclamaient, mais envoya la consomption dans leurs organes.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Ils furent jaloux de Moïse dans le camp, d’Aaron, le saint de l’Eternel.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
La terre, s’entrouvrant, engloutit Dathan, elle se referma sur la bande d’Abirâm.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Un feu consuma leur troupe, une flamme embrasa les impies.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Ils fabriquèrent un veau près du Horeb, et se prosternèrent devant une idole en fonte.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
Ils troquèrent ainsi leur gloire contre l’effigie d’un bœuf qui broute l’herbe.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Ils avaient oublié Dieu, leur sauveur, qui avait accompli de si grandes choses en Egypte,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
des merveilles dans le pays de Cham, de formidables prodiges près de la mer des Joncs.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Il parlait de les anéantir, si Moïse, son élu, ne se fût placé sur la brèche devant lui, pour détourner sa colère prête à tout détruire.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Puis ils montrèrent du dédain pour un pays délicieux, n’ayant pas foi en sa parole.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
Ils murmurèrent dans leurs tentes, n’écoutèrent point la voix de l’Eternel;
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
et il leva la main contre eux pour jurer qu’il les ferait succomber dans le désert,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
qu’il rejetterait leurs descendants parmi les nations, et les disperserait dans leurs contrées.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Ils se prostituèrent à Baal-Peor, et mangèrent des sacrifices offerts à des dieux inanimés.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Ils déchaînèrent la colère par leurs actes, et un fléau fit irruption parmi eux.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Mais Phinéas se leva pour faire justice, et le fléau cessa de sévir.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Cette action lui fut comptée comme un mérite, d’âge en âge, jusque dans l’éternité.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Ils suscitèrent le courroux divin aux eaux de Meriba, et il advint du mal à Moïse à cause d’eux.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Car ils furent rebelles à l’esprit de Dieu, et ses lèvres prononcèrent l’arrêt.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
Ils n’exterminèrent point les nations que l’Eternel leur avait désignées.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Ils se mêlèrent aux peuples et s’inspirèrent de leurs coutumes,
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
adorant leurs idoles, qui devinrent pour eux un piège.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Ils sacrifièrent leurs fils et leurs filles aux démons,
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
répandirent du sang innocent, le sang de leurs fils et de leurs filles, qu’ils immolaient aux idoles de Canaan, et le pays fut déshonoré par des flots de sang.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Ils se souillèrent par leurs œuvres, et leurs actes furent une longue prostitution.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
La colère de l’Eternel s’alluma contre son peuple, et il prit en horreur son héritage.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
Il les livra au pouvoir des nations, ceux qui les haïssaient devinrent leurs maîtres.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Leurs ennemis les opprimèrent, et les firent plier sous leur joug.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Maintes fois Dieu les délivra, mais ils redevenaient rebelles de propos délibéré, et tombaient en décadence par leurs fautes.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Il devenait attentif à leur détresse, quand il entendait leurs supplications,
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
se souvenant, pour leur bien, de son alliance, et se laissant fléchir dans son infinie miséricorde.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Il émouvait la pitié en leur faveur chez tous ceux qui les retenaient captifs.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Viens à notre secours, Eternel, notre Dieu, rassemble-nous d’entre les nations, pour que nous rendions hommage à ton saint nom, et cherchions notre gloire dans tes louanges.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Béni soit l’Eternel, le Dieu d’Israël, d’éternité en éternité, et que le peuple tout entier dise: "Amen! Alléluia!"