< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Praise ye the LORD! O give thanks to the LORD, for he is good; For his mercy endureth for ever!
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Who can utter the mighty deeds of the LORD? Who can show forth all his praise?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Happy are they who have regard to justice, Who practise righteousness at all times!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Remember me, O LORD! with the favor promised to thy people; O visit me with thy salvation!
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
That I may see the prosperity of thy chosen, That I may rejoice in the joy of thy people, That I may glory with thine inheritance!
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
We have sinned with our fathers; We have committed iniquity; we have done wickedly.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Our fathers in Egypt did not regard thy wonders; They remembered not the multitude of thy mercies; But rebelled at the sea, the Red sea.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Yet he saved them for his own name's sake. That he might make his mighty power to be known.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
He rebuked the Red sea, and it was dried up, And he led them through the deep as through a desert.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
He saved them from the hand of him that hated them, And redeemed them from the hand of the enemy.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
The waters covered their enemies; There was not one of them left.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Then believed they his words, And sang his praise.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
But they soon forgot his deeds, And waited not for his counsel.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
They gave way to appetite in the wilderness, And tempted God in the desert;
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
And he gave them their request, But sent upon them leanness.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
They also envied Moses in the camp, And Aaron, the holy one of the LORD.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Then the earth opened, and swallowed up Dathan, And covered the company of Abiram,
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
And a fire was kindled in their company; The flames burned up the wicked.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
They made a calf in Horeb, And worshipped a molten image;
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
They changed their God of glory Into the image of a grass-eating ox.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
They forgot God, their saviour, Who had done such great things in Egypt,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Such wonders in the land of Ham. Such terrible things at the Red sea.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Then he said that he would destroy them; Had not Moses, his chosen, stood before him in the breach, To turn away his wrath, that he might not destroy them.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
They also despised the pleasant land, And believed not his word;
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
But murmured in their tents, And would not hearken to the voice of the LORD.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
Then he lifted up his hand against them, And swore that he would make them fall in the wilderness;
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
That he would overthrow their descendants among the nations, And scatter them in the lands.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
They also gave themselves to the worship of Baal-peor, And ate sacrifices offered to lifeless idols.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
Thus they provoked his anger by their practices, And a plague broke in upon them.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Then stood up Phinehas, and executed judgment, And the plague was stayed.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
And this was counted to him for righteousness, To all generations for ever.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
They provoked him also at the waters of Meribah [[strife]], And evil befell Moses on their account.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
For they provoked his spirit, So that he spake inconsiderately with his lips.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
They did not destroy the nations, As Jehovah had commanded them.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
They mingled themselves with the peoples, And learned their practices.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
They even worshipped their idols, Which became to them a snare.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Their sons and their daughters they sacrificed to demons,
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
And shed innocent blood, The blood of their own sons and daughters, Whom they sacrificed to the idols of Canaan; And the land was polluted with blood.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
Thus they defiled themselves with their works, And played the harlot with their practices.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Then burned the anger of the LORD against his people, So that he abhorred his own inheritance.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
And he gave them into the hand of the nations, And they who hated them ruled over them.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Their enemies oppressed them, And they were bowed down under their hand.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Many times did he deliver them; But they provoked him by their devices, And they were brought low for their iniquities.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Yet, when he heard their cries, He had regard to their affliction;
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
He remembered his covenant with them, And repented according to the greatness of his mercy,
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
And caused them to find pity Among all that carried them captive.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Save us, O Jehovah, our God! and gather us from among the nations, That we may give thanks to thy holy name, And glory in thy praise!
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
[Blessed be Jehovah, the God of Israel, From everlasting to everlasting! And let all the people say, Amen! Praise ye Jehovah!]

< Zabura 106 >