< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Alleluia. Give glory to the Lord, for he is good: for his mercy endureth for ever.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Who shall declare the powers of the Lord? who shall set forth all his praises?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Blessed are they that keep judgment, and do justice at all times.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Remember us, O Lord, in the favour of thy people: visit us with thy salvation.
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
That we may see the good of thy chosen, that we may rejoice in the joy of thy nation: that thou mayst be praised with thy inheritance.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
We have sinned with our fathers: we have acted unjustly, we have wrought iniquity.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Our fathers understood not thy wonders in Egypt: they remembered not the multitude of thy mercies: And they provoked to wrath going up to the sea, even the Red Sea.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
And he saved them for his own name’s sake: that he might make his power known.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
And he rebuked the Red Sea, and it was dried up: and he led them through the depths, as in a wilderness.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
And he saved them from the hand of them that hated them: and he redeemed them from the hand of the enemy.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
And the water covered them that afflicted them: there was not one of them left.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
And they believed his words: and they sang his praises.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
They had quickly done, they forgot his works: and they waited not for his counsels.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
And they coveted their desire in the desert: and they tempted God in the place without water.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
And he gave them their request: and sent fulness into their souls.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
And they provoked Moses in the camp, Aaron the holy one of the Lord.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
The earth opened and swallowed up Dathan: and covered the congregation of Abiron.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
And a fire was kindled in their congregation: the flame burned the wicked.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
They made also a calf in Horeb: and they adored the graven thing.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
And they changed their glory into the likeness of a calf that eateth grass.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
They forgot God, who saved them, who had done great things in Egypt,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Wondrous works in the land of Cham: terrible things in the Red Sea.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
And he said that he would destroy them: had not Moses his chosen stood before him in the breach: To turn away his wrath, lest he should destroy them.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
And they set at nought the desirable land. They believed not his word,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
And they murmured in their tents: they hearkened not to the voice of the Lord.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
And he lifted up his hand over them: to overthrow them in the desert;
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
And to cast down their seed among the nations, and to scatter them in the countries.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
They also were initiated to Beelphegor: and ate the sacrifices of the dead.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
And they provoked him with their inventions: and destruction was multiplied among them.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Then Phinees stood up, and pacified him: and the slaughter ceased.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
And it was reputed to him unto justice, to generation and generation for evermore.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
They provoked him also at the waters of contradiction: and Moses was afflicted for their sakes:
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Because they exasperated his spirit. And he distinguished with his lips.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
They did not destroy the nations of which the Lord spoke unto them.
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
And they were mingled among the heathens, and learned their works:
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
And served their idols, and it became a stumblingblock to them.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
And they sacrificed their sons, and their daughters to devils.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
And they shed innocent blood: the blood of their sons and of their daughters which they sacrificed to the idols of Chanaan. And the land was polluted with blood,
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
And was defiled with their works: and they went aside after their own inventions.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
And the Lord was exceedingly angry with his people: and he abhorred his inheritance.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
And he delivered them into the hands of the nations: and they that hated them had dominion over them.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
And their enemies afflicted them: and they were humbled under their hands:
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Many times did he deliver them. But they provoked him with their counsel: and they were brought low by their iniquities.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
And he saw when they were in tribulation: and he heard their prayer.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
And he was mindful of his covenant: and repented according to the multitude of his mercies.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
And he gave them unto mercies, in the sight of all those that had made them captives.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Save us, O Lord, our God: and gather us from among nations: That we may give thanks to thy holy name, and may glory in thy praise.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Blessed be the Lord the God of Israel, from everlasting to everlasting: and let all the people say: So be it, so be it.

< Zabura 106 >