< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Hallelujah! Give thanks to the LORD, for He is good; His loving devotion endures forever.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Who can describe the mighty acts of the LORD or fully proclaim His praise?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Blessed are those who uphold justice, who practice righteousness at all times.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Remember me, O LORD, in Your favor to Your people; visit me with Your salvation,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
that I may see the prosperity of Your chosen ones, and rejoice in the gladness of Your nation, and give glory with Your inheritance.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
We have sinned like our fathers; we have done wrong and acted wickedly.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Our fathers in Egypt did not grasp Your wonders or remember Your abundant kindness; but they rebelled by the sea, there at the Red Sea.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Yet He saved them for the sake of His name, to make His power known.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
He rebuked the Red Sea, and it dried up; He led them through the depths as through a desert.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
He saved them from the hand that hated them; He redeemed them from the hand of the enemy.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
The waters covered their foes; not one of them remained.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
Then they believed His promises and sang His praise.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Yet they soon forgot His works and failed to wait for His counsel.
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
They craved intensely in the wilderness and tested God in the desert.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
So He granted their request, but sent a wasting disease upon them.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
In the camp they envied Moses, as well as Aaron, the holy one of the LORD.
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
The earth opened up and swallowed Dathan; it covered the assembly of Abiram.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Then fire blazed through their company; flames consumed the wicked.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
At Horeb they made a calf and worshiped a molten image.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
They exchanged their Glory for the image of a grass-eating ox.
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
They forgot God their Savior, who did great things in Egypt,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
wondrous works in the land of Ham, and awesome deeds by the Red Sea.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
So He said He would destroy them— had not Moses His chosen one stood before Him in the breach to divert His wrath from destroying them.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
They despised the pleasant land; they did not believe His promise.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
They grumbled in their tents and did not listen to the voice of the LORD.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
So He raised His hand and swore to cast them down in the wilderness,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
to disperse their offspring among the nations and scatter them throughout the lands.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
They yoked themselves to Baal of Peor and ate sacrifices offered to lifeless gods.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
So they provoked the LORD to anger with their deeds, and a plague broke out among them.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
But Phinehas stood and intervened, and the plague was restrained.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
It was credited to him as righteousness for endless generations to come.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
At the waters of Meribah they angered the LORD, and trouble came to Moses because of them.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
For they rebelled against His Spirit, and Moses spoke rashly with his lips.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
They did not destroy the peoples as the LORD had commanded them,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
but they mingled with the nations and adopted their customs.
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
They worshiped their idols, which became a snare to them.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
They sacrificed their sons and their daughters to demons.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
They shed innocent blood— the blood of their sons and daughters, whom they sacrificed to the idols of Canaan, and the land was polluted with blood.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
They defiled themselves by their actions and prostituted themselves by their deeds.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
So the anger of the LORD burned against His people, and He abhorred His own inheritance.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
He delivered them into the hand of the nations, and those who hated them ruled over them.
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
Their enemies oppressed them, and subdued them under their hand.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Many times He rescued them, but they were bent on rebellion and sank down in their iniquity.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
Nevertheless He heard their cry; He took note of their distress.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
And He remembered His covenant with them, and relented by the abundance of His loving devotion.
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
He made them objects of compassion to all who held them captive.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Save us, O LORD our God, and gather us from the nations, that we may give thanks to Your holy name, that we may glory in Your praise.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Blessed be the LORD, the God of Israel, from everlasting to everlasting. Let all the people say, “Amen!” Hallelujah!