< Zabura 106 >

1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Halleluja! Lov Herren, thi han er god, thi hans miskundhed varer evindelig!
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Hvo kan opregne Herrens vældige gerninger, finde ord til at kundgøre al hans pris?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Salige de, der holder på ret, som altid øver retfærdighed!
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Husk os, Herre, når dit folk finder nåde, lad os få godt af din frelse,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
at vi må se dine udvalgtes lykke, glæde os ved dit folks glæde og med din arvelod prise vor lykke!
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Vi syndede som vore Fædre, handlede ilde og gudløst.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Vore Fædre i Ægypten ænsede ej dine Undere, kom ikke din store Miskundhed i Hu, stod den Højeste imod ved det røde Hav.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
Dog frelste han dem for sit Navns Skyld, for at gøre sin Vælde kendt;
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
han trued det røde Hav, og det tørrede ud, han førte dem gennem Dybet som gennem en Ørk;
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
han fried dem af deres Avindsmænds Hånd og udløste dem fra Fjendens Hånd;
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
Vandet skjulte dem, som trængte dem, ikke een blev tilbage af dem;
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
da troede de på hans Ord og kvad en Sang til hans Pris.
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Men de glemte snart hans Gerninger, biede ej på hans Råd;
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
de grebes af Attrå i Ørkenen, i Ødemarken fristed de Gud;
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
så gav han dem det, de kræved og sendte dem Lede i Sjælen.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
De bar Avind mod Moses i Lejren, mod Aron, HERRENs hellige;
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Jorden åbned sig, slugte Datan, lukked sig over Abirams Flok;
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
Ilden rasede i deres Flok, Luen brændte de gudløse op.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
De lavede en Kalv ved Horeb og tilbad det støbte Billed;
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
de byttede deres Herlighed bort for et Billed af en Okse, hvis Føde er Græs;
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
de glemte Gud, deres Frelser, som øvede store Ting i Ægypten,
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
Undere i Kamiternes Land, frygtelige Ting ved det røde Hav.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Da tænkte han på at udrydde dem, men Moses, hans udvalgte Mand, stilled sig i Gabet for hans Åsyn for at hindre, at hans Vrede lagde øde.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
De vraged det yndige Land og troede ikke hans Ord,
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
men knurrede i deres Telte og hørte ikke på HERREN;
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
da løfted han Hånden og svor at lade dem falde i Ørkenen,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
splitte deres Sæd blandt Folkene, sprede dem rundt i Landene.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
De holdt til med Ba'al-Peor og åd af de dødes Ofre;
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
de krænked ham med deres Gerninger, og Plage brød løs iblandt dem.
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Da stod Pinehas frem og holdt Dom, og Plagen blev bragt til at standse,
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
og det regnedes ham til Retfærdighed fra Slægt til Slægt, evindelig.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
De vakte hans Vrede ved Meribas Vand, og for deres Skyld gik det Moses ilde;
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
thi de stod hans Ånd imod, og han talte uoverlagte Ord.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
De udryddede ikke de Folk, som HERREN havde sagt, de skulde,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
med Hedninger blandede de sig og gjorde deres Gerninger efter;
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
deres Gudebilleder dyrkede de, og disse blev dem en Snare;
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
til Dæmonerne ofrede de, og det både Sønner og Døtre;
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
de udgød uskyldigt Blod, deres Sønners og Døtres Blod, som de ofred til Kana'ans Guder, og Landet blev smittet ved Blod;
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
de blev urene ved deres Gerninger, bolede ved deres idrætter.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Da blev HERREN vred på sit Folk og væmmedes ved sin Arv;
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
han gav dem i Folkenes Hånd, deres Avindsmænd blev deres Herrer;
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
deres Fjendervoldte dem Trængsel, de kuedes under deres Hånd.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Han frelste dem Gang på Gang, men de stod egensindigt imod og sygnede hen i Brøden;
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
dog så han til dem i Trængslen, så snart han hørte dem klage;
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
han kom sin Pagt i Hu og ynkedes efter sin store Miskundhed;
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
han lod dem finde Barmhjertighed hos alle, der tog dem til Fange.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Frels os, HERRE vor Gud, du samle os sammen fra Folkene, at vi må love dit hellige Navn, med Stolthed synge din Pris.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Lovet være HERREN, Israels Gud, fra Evighed og til Evighed! Og alt Folket svare Amen!

< Zabura 106 >