< Zabura 106 >
1 Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
Halelujah. Oslavujte Hospodina, nebo dobrý jest, nebo na věky milosrdenství jeho.
2 Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
Kdo může vymluviti nesmírnou moc Hospodinovu, a vypraviti všecku chválu jeho?
3 Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
Blahoslavení, kteříž ostříhají soudu, a činí spravedlnost každého času.
4 Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
Pamatuj na mne, Hospodine, pro milost k lidu svému, navštěv mne spasením svým,
5 don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
Abych užíval dobrých věcí s vyvolenými tvými, a veselil se veselím národu tvého, a chlubil se spolu s dědictvím tvým.
6 Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
Zhřešili jsme i s otci svými, neprávě jsme činili, a bezbožnost páchali.
7 Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
Otcové naši v Egyptě nerozuměli předivným skutkům tvým, aniž pamatovali na množství milosrdenství tvých, ale odporni byli při moři, při moři Rudém.
8 Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
A však vysvobodil je pro jméno své, aby v známost uvedl moc svou.
9 Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
Nebo přimluvil moři Rudému, a vyschlo; i provedl je skrze hlubiny, jako po poušti.
10 Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
A tak zachoval je od ruky toho, jenž jich nenáviděl, a vyprostil je z ruky nepřítele.
11 Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
V tom přikryly vody ty, kteříž je ssužovali, nezůstalo ani jednoho z nich.
12 Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
A ačkoli věřili slovům jeho, a zpívali chválu jeho,
13 Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
Však rychle zapomenuli na skutky jeho, a nečekali na radu jeho;
14 A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
Ale jati jsouce žádostí na poušti, pokoušeli Boha silného na pustinách.
15 Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
I dal jim, čehož se jim chtělo, a však dopustil hubenost na život jejich.
16 A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
Potom, když horlili proti Mojžíšovi v vojště, a Aronovi, svatému Hospodinovu,
17 Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
Otevřevši se země, požřela Dátana, a přikryla zběř Abironovu.
18 Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
A roznícen byl oheň na rotu jejich, plamen spálil bezbožníky.
19 A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
Udělali i tele na Orébě, a skláněli se slitině.
20 Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
A změnivše slávu svou v podobiznu vola, jenž jí trávu,
21 Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
Zapomněli na Boha silného, spasitele svého, kterýž činil veliké věci v Egyptě.
22 mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
A předivné v zemi Chamově, přehrozné při moři Rudém.
23 Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
Pročež řekl, že je vypléní, kdyby se byl Mojžíš, vyvolený jeho, nepostavil v té mezeře před ním, a neodvrátil prchlivosti jeho, aby nehubil.
24 Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
Za tím zošklivili sobě zemi žádanou, nevěříce slovu jeho.
25 Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
A repcíce v staních svých, neposlouchali hlasu Hospodinova.
26 Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
A protož pozdvihl ruky své proti nim, aby je rozmetal po poušti,
27 ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
A aby rozptýlil símě jejich mezi pohany, a rozehnal je do zemí.
28 Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
Spřáhli se také byli s modlou Belfegor, a jedli oběti mrch.
29 suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
A tak dráždili Boha skutky svými, až se na ně obořila rána,
30 Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
Až se postavil Fínes, a pomstu vykonal, i přetržena jest rána ta.
31 An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
Což jest mu počteno za spravedlnost od národu do pronárodu, a až na věky.
32 A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
Opět ho byli popudili při vodách sváru, až se i Mojžíšovi zle stalo pro ně.
33 saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
Nebo k hořkosti přivedli ducha jeho, a pronesl ji rty svými.
34 Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
K tomu nevyplénili ani národů těch, o kterýchž jim byl Hospodin poručil,
35 amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
Ale směšujíce se s těmi národy, naučili se skutkům jejich,
36 Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
A sloužili modlám jejich, kteréž jim byly osídlem.
37 Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
Obětovali zajisté syny své a dcery své ďáblům.
38 Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
A vylili krev nevinnou, krev synů svých a dcer svých, kteréž obětovali trapidlům Kananejským, tak že poškvrněna jest země těmi vraždami.
39 Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
I zmazali se skutky svými, a smilnili činy svými.
40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
Protož rozpáliv se v prchlivosti Hospodin na lid svůj, v ošklivost vzal dědictví své.
41 Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
A vydal je v ruce pohanů. I panovali nad nimi ti, jenž je v nenávisti měli,
42 Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
A utiskali je nepřátelé jejich, tak že sníženi jsou pod ruku jejich.
43 Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
Mnohokrát je vysvobozoval, oni však popouzeli ho radou svou, pročež potlačeni jsou pro nepravost svou.
44 Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
A však patřil na úzkost jejich, a slyšel křik jejich.
45 saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
Nebo se rozpomenul na smlouvu svou s nimi, a želel toho podlé množství milosrdenství svých,
46 Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
Tak že naklonil k nim lítostí všecky, kteříž je u vězení drželi.
47 Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
Zachovej nás, Hospodine Bože náš, a shromažď nás z těch pohanů, abychom slavili jméno tvé svaté, a chlubili se v chvále tvé.
48 Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.
Požehnaný Hospodin Bůh Izraelský od věků až na věky. Na to rciž všecken lid: Amen, Halelujah.