< Zabura 105 >

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
Tacken HERREN, åkallen hans namn, gören hans gärningar kunniga bland folken.
2 Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
Sjungen till hans ära, lovsägen honom, talen om alla hans under.
3 Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
Berömmen eder av hans heliga namn; glädje sig av hjärtat de som söka HERREN.
4 Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
Frågen efter HERREN och hans makt, söken hans ansikte beständigt.
5 Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
Tänken på de underbara verk som han har gjort, på hans under och hans muns domar,
6 Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
I Abrahams, hans tjänares, säd, I Jakobs barn, hans utvalda.
7 Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
Han är HERREN, vår Gud; över hela jorden gå hans domar.
8 Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
Han tänker evinnerligen på sitt förbund, intill tusen släkten på vad han har stadgat,
9 alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
på det förbund han slöt med Abraham och på sin ed till Isak.
10 Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
Han fastställde det för Jakob till en stadga, för Israel till ett evigt förbund;
11 “Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
han sade: "Åt dig vill jag giva Kanaans land, det skall bliva eder arvedels lott."
12 Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
Då voro de ännu en liten hop, de voro ringa och främlingar därinne.
13 suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
Och de vandrade åstad ifrån folk till folk, ifrån ett rike bort till ett annat.
14 Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
Han tillstadde ingen att göra dem skada, han straffade konungar för deras skull:
15 “Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
"Kommen icke vid mina smorda, och gören ej mina profeter något ont."
16 Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
Och när han bjöd hungersnöd komma över landet och fördärvade allt deras livsuppehälle,
17 ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
då sände han åstad en man framför dem: Josef blev såld till träl.
18 Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
Man slog hans fötter i bojor, i järn fick han ligga fjättrad,
19 sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
till den tid då hans ord uppfylldes, då HERRENS tal bevisade hans oskuld.
20 Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
Då sände konungen och lät släppa honom lös, folkens behärskare gav honom fri.
21 Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
Han satte honom till herre över sitt hus, till att råda över all hans egendom;
22 don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
han skulle binda hans furstar efter sin vilja och lära hans äldste vishet.
23 Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
Och Israel kom till Egypten, Jakob blev en gäst i Hams land.
24 Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
Och HERREN gjorde sitt folk mycket fruktsamt och mäktigare än dess ovänner voro,
25 waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
de vilkas hjärtan han vände till att hata hans folk, till att lägga onda råd mot hans tjänare.
26 Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
Han sände Mose, sin tjänare, och Aron, som han hade utvalt.
27 Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
De gjorde hans tecken ibland dem och under i Hams land.
28 Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
Han sände mörker och lät allt bliva mörkt; och de stodo icke emot hans ord.
29 Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
Han förvandlade deras vatten till blod och lät så deras fiskar dö.
30 Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
Deras land kom att vimla av paddor, ända in i deras konungars kamrar.
31 Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
Han bjöd, och flugsvärmar kommo, mygg i hela deras land.
32 Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
Han gav dem hagel för regn, eldslågor sände han i deras land.
33 ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
Och han slog deras vinträd och fikonträd och bröt sönder träden i deras land.
34 Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
Han bjöd, och gräshoppor kommo, och gräsmaskar i tallös mängd.
35 suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
De åto upp alla örter i deras land, de åto upp frukten på deras mark.
36 Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
Och han slog allt förstfött i deras land, förstlingen av all deras kraft.
37 Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
Så förde han dem ut, med silver och guld, och i hans stammar var ingen som stapplade.
38 Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
Egyptierna gladde sig, när de drogo ut; ty förskräckelse för Israel hade fallit över dem.
39 Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
Han bredde ut ett moln till skygd, och en eld för att lysa om natten.
40 Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
De begärde, då lät han vaktlar komma, och med bröd från himmelen mättade han dem.
41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
Han öppnade klippan, och vatten flödade; det gick genom öknen såsom en ström.
42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
Ty han tänkte på sitt heliga ord, på sin tjänare Abraham.
43 Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
Så förde han ut sitt folk med fröjd, med jubel dem som han hade utvalt.
44 ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
Han gav åt dem hedningarnas länder, och folkens förvärv fingo de till besittning,
45 don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.
för att de skulle hålla hans stadgar och taga hans lagar i akt. Halleluja!

< Zabura 105 >